Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Kotu A Birnin Tarayya Abuja Ta Bada Belin Tsohon Minista Abubakar Malami
Published: December 24, 2025 at 11:00 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Kotun FCT Abuja ta bayar da belin wucin gadi ga Abubakar Malami, ta dage sauraron shari’a zuwa 5 ga Janairu

Babbar Kotun Babban Birnin Tarayya (FCT) da ke Abuja Najeriya ta bayar da belin wucin gadi ga tsohon Babban Lauyan kasar kuma Ministan Shari’a, Abubakar Malami, a shari’ar da Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa (EFCC) ke gabatarwa a kansa.

Mai shari’a Bello Kawu ne ya yanke wannan hukunci a ranar Talata, 23 ga Disamba, 2025, yayin sauraron ƙarar mai lamba M/17220/2025.

Kotun ta ce an bayar da belin ne bisa sharuddan da EFCC ta riga ta gindaya tun farko, waɗannan sun haɗa da mika fasfo ɗin tafiyar ƙasashen waje na Malami, tare da cike takardun beli daga mutane biyu masu tsaya masa.

Mutanen da za su tsaya masa su ne Daraktan Janar na Hukumar Tallafin Shari’a ta Ƙasa (Legal Aid Council) da kuma ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar mazabar Augie/Argungu.

Mai shari’a Kawu ya kuma sake dubawa tare da farfaɗo da sharuɗɗan belin da aka riga aka cika tun 28 ga Nuwamba, 2025, ciki har da mika fasfo da kuma gabatar da mutanen da za su tsaya masa.

Kotun ta bayyana cewa an bayar da belin wucin gadin ne bisa dalilin tsananin wahala ta musamman, har zuwa lokacin da za a saurara kuma a yanke hukunci kan babbar ƙarar da ke gaban kotu.

An dage sauraron shari’ar zuwa 5 ga Wata Janairu, 2026, domin jin ƙarar a hukumance.

Najeriya

Post navigation

Previous Post: An Gano Kwale-Kwalen Fir’auna A Birnin Masar
Next Post: Gwamnatin Jamhuriyar Nijar Na Kokarin Inganta Harkokin Noman Kasar

Karin Labarai Masu Alaka

Dangote Ya Bukaci ICPC Ta Binciki Shugaban NMDPRA Najeriya
Hukumar NDLEA Ta Kama Wata Mata Da cikin Bogi Na ƙwaya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Gwamnatin Kano Ta Rufe Gidajen Bukukuwa Da Shakatawa Labarai
Burkina Faso Ta Sako ‘Yan Najeriya 11 Najeriya
Rundunar Operation Hadinkai Sunyi Nasara Akan ISWAP Da Boko Haram Najeriya
Ganduje Ya Nisanta Kansa Da Batan Dadiyata Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ‘Yan Uwa Musulmi A Jihar Gombe Sunyi Allah Wadai Da Kisan Ayatollah Khomeini
  • An Samu Kaburbura Biyu Dauke Da Gawarwaki 173 A Kasar Kwango
  • Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi
  • Karancin Iskar Gas Kalubale Ne Ga Wutar Lantarki
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • ‘Yan Ta’adda Sun Hallaka Malaman Makaranta A Tilabery Afrika
  • Najeriya Ta Kai Wasan Kusa Da Na Karshe A Wasan Dambe Na Matasan Afirka Wasanni
  • Shugaban Mulkin Soja A Mali Ya Kirkiro Mukami Kamar Minista Afrika
  • An Kubutar Da ‘Yan Matan Sakandire Su 24 Na Jihar Kebbi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Trump Yayi Barazanar Goyon Bayan Hari Akan Kasar Iran Labarai
  • Shugaba Trump Yace Amurka Ce Zata Rika Gudanar Da Harkokin Kasar Venezuela Amurka
  • Jirgi Marar Matuki Yayi Ajalin A Kallah Mambobin M23 9 Tare Da Kashe Kakakin Rundunar Afrika
  • Ana Cigaba Da Tattaunawa Tsakanin Trump Da Zelensky Domin Tsagaita Wuta A Ukraine Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.