Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Kotu A Kasar Faransa Ta Daure Lumbala Shekaru 30 Bisa Laifin Cin Zarafi
Published: December 17, 2025 at 8:40 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Wata kotu a kasar Faransa ta yanke hukuncin daurin shekaru 30 a gidan kurkuku a kan tsohon madugun ‘yan tawayen Kwango ta Kinshasa, Roger Lumbala, wanda ta samu da laifuffukan cin zarafin bil Adama a lokacin yakin Kwango na biyu.

‘Yan rajin ganin an hukumta masu aikata irin wadannan laifuffuka a gadin duniya sun yaba da wannan hukunci a zaman babban ci gaba na hukumta masu hannu a wannan yakin da ya kashe miliyoyin mutane.

A lokacin da yake bayyana hukuncin, alkalin wannan kotu dake birnin Paris, Marc Sommerer, yace Lumbala ya aikata ko ya bada umurnin aikatawa, ko ya tallafa wajen aikata munanan laifuffuka da kashe-kashe da fyade, da gana azaba, da bautarwa da sata da wawusa ko lalata dukiyoyi.

Wadannan laifuffukan da aka tuhumi Lumbala da aikatawa suna da alaka da wani farmakin da wata kungiyarsa mai samun goyon bayan kasar uganda a lokacin, ta kai a shekarun 2002 da kuma 2003 a arewa maso gabashin Kwango.

Sun kai hare-haren ne a kan ‘yan kabilun Nande da Bambuti wadanda suka zarga da laifin goyon bayan wata kungiyar daban ta sojojin sa kai a yankin.

An gudanar da yakin Kwango na biyu daga shekarar 1998 zuwa 2003. Kasashe har guda 9 suka tsoma baki da hannu a wannan yaki, kuma an kashe mutane fiye da miliyan 5, cikinsu har da wadanda suka mutu a sanadin yunwa da kuma cututtuka.

Labarai

Post navigation

Previous Post: Wani Bayahude Ya Harbe Bafalatsine Dan Shekaru 16
Next Post: Gwamnatin Jihar Yobe: Ana Cin Zarafin Fursunoni A Gidan Gyaran Halin Potiskum

Karin Labarai Masu Alaka

Gobara Ta Lalata Shaguna Da Gidajen Abinci A Gombe Labarai
Hawan Sallah A Jihar Katsina Afrika
Nan Gaba Kadan Kwallon Badminton Zata Samu Karbuwa Kamar Kwallon Kafa A Duniya Labarai
Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Rasha: Tura Sojojin Birtaniya Ukraine Zai Kara Ta’azzara Yaki Labarai
Hawan Nasarawa A Jihar Kano Afrika
Gwamnan Jihar Kebbi Ya Amince Da Biyan Hakkokin Tsofin Ma’aikata 800 Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Wani Dan Ta’adda Ya Hallaka ‘Yan Makaranta A Kasar Uganda
  • Sakataren Tsaron Amurka Ya Kori Shugaban Sojin Kasar
  • Kwararru Sun Nuna Damuwa Game Da Yakin Iran
  • Za’a Kada Kuri’a A Kwamitin Tsaro Na MDD Kan Yaki
  • Kasashen Da Dama Na Neman Hanyar Cigaba Da Dakon Makamashi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Hukumar DSS Ta Sake Kama Abubakar Malami Labarai
  • Ana Cigaba Da Samun Hare Hare Da Jiragen Marasa Matuki A Sudan Labarai
  • Gwamna Abba Gida-Gida Na Dari-Darin Shiga APC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • INEC: Akwai Yiwuwar Dage Zaben 2027 Saboda Azumi Labarai
  • Channels TV: Ta Yi Rashin Hazikin Dan Jarida Mr Khani Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Tana Saka Ido Akan Matsalolin Gabas Ta Tsakiya Afrika
  • Gwamnatin Gombe Ta Raba Naira Miliyan 14 Ga Iyalen ‘Yan Jaridan Da Suka Rasu Najeriya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.