Kungiyar HPV ta jihar Gombe ta shirya wani gangamin wayar da kan al’umma, inda ta hada ‘yan jarida, ma’aikatan lafiya, masana ilimi, shugabannin al’umma da sauran masu ruwa da tsaki domin tunkarar barazanar karuwar cutar daji a jihar.
Da yake jawabi a wajen taron, Farfesa Muhammad Manga ya bukaci mahalarta su kirkiro dabaru masu amfani domin hana yaduwar cutar daji, musamman cutar sankarar mahaifa, da kuma yadda za a magance sauran nau’o’in cutar a cikin al’umma.
Ya bayyana cewa an hada bangarori daban-daban cikin shirin ne da gangan, musamman mambobin Kungiyar ‘Yan Jarida ta Najeriya, domin inganta tattaunawa da gano hanyoyin magance matsalolin cutar daji.
Farfesa Manga ya yaba wa mahalarta taron bisa jajircewarsu, yana mai jaddada cewa ana iya warkar da cutar daji idan aka gano ta da wuri. Ya kuma bukaci jama’a da su gaggauta neman kulawar likita idan sun lura da wasu sauye-sauye ko alamomi da ba su saba ba, tare da karfafa musu gwiwa su yada wannan sakon wayar da kai a cikin al’ummominsu.

Sauran masu jawabi, ciki har da shugabar taron, Dakta Halima Usman Farouk, Farfesa Danladi Adamu Bojude da Ferfesa Aliyu Lawal na Asibitin Koyarwa na Tarayya da ke Gombe, da kuma shugabannin al’umma Musa Mustafa da Danimoh Mustafa, sun jaddada bukatar kara hadin gwiwa tsakanin ‘yan jarida, ma’aikatan lafiya da sauran masu ruwa da tsaki domin yakar cutar daji yadda ya kamata.
Sun bayyana wasu daga cikin nau’o’in cutar daji da suka fi yawaita a jihar da suka hada da na mama, huhu, mafitsara ta maza, mahaifa, hanta, ciki, pankiriyas, koda, mafitsara, fata, kwakwalwa, ovaries, mahaifa ta mata da kuma esophagus.
Masu jawabin sun bukaci jama’a da su rika anfani da ayyukan kiwon lafiya da ake da su ta hanyar yin gwaje-gwaje akai-akai. Wadanda aka gano suna dauke da cutar an shawarce su da su nemi magani da wuri, yayin da sauran kuma aka karfafa musu gwiwa su yi allurar rigakafi inda ya dace.

Kungiyar ta sake jaddada kudirinta na kara fadada shirye-shiryen wayar da kai da kuma inganta samun damar ayyukan rigakafi domin rage mace-macen da ke da alaka da cutar daji a Jihar Gombe.


