A ranar Laraba ne kungiyar kwallon kafar mata ta Iran ta tsallaka kan iyakar Turkiyya zuwa Iran domin kammala tattaki na dawowa daga kasar Ostiraliya, bayan da wasu mambobi biyar suka janye neman mafakar da suka yi a can.
Ostiraliya ta ba da bizar jin kai ga ‘yan wasa shida da wani ma’aikacin tallafi daya bayan da suka nemi mafaka, inda suka ce suna fargabar za a iya tsananta musu idan suka koma Iran.
An nuna damuwa game da tsaron lafiyarsu a lokacin da ‘yan wasa da dama suka kasa rera taken kasar a gasar cin kofin Asiya ta mata a farkon watan nan bayan da Amurka da Isra’ila suka kaddamar da yaki da Iran. Gidan talabijin din kasar Iran ya yi musu lakabi da “masu cin amana a lokacin yaki”.
Tawagar wacce ta tashi zuwa Istanbul a ranar Talata, ta tashi zuwa Igdir da ke gabashin Turkiyya da safiyar yau.


