Dubban magoya bayan dan hamayya a Afirka ta kudu, Julius Malema ne suka hallara a harabar wani kotu, suna dakon hukuncin da za’a yanke masa saboda samunsa da laifin harba Bindiga a wani gangami. Lamarin ya auku ne a shekara ta 2018.

A duk mataki a daukaka karar da yayi kotuan ba su canza hukuncin daurin da ya zarce wata 12 da aka yanke masa tunda hukuncin farko ba, mataki da zai hana shugaban jam’iyyar EFF a takaice, watau Economic Freedom Fighter da turanci, shi Julius malema, ci gaba da zama wakili a majalisar dokokin kasar. Jam’iyyar tana da farin jini musamman ga matasa wadanda suke sukar lamirin gwamnati gameda matsalolin ci gaba da nuna wariya a kasar tun bayan kawo karshen mulkin wariya ta tsiraru farar fata a kasar.
Malema yana fuskantar daurin shekaru da zasu kai 15, amma yana iya samun sassauci idan kotu ta gamsu akwai hujjoji kwarara gameda abunda ya aikata.
Malema dan ashekaru 44 da haifuwa, kotu ta same shi laifuffuka da suka hada da mallakar binidga ba bisa doka ba, daharba bindiga a bainar jama’a. Dan majaisar yaki ya amsa tuhuma da aka yi masa, yana mai cewa binidgar ta roba ce.


