Magoya bayan Darikar tijjaniya a Najeriya sun yi barazanar kauracewa Babban zaben Kasar mai zuwa Idan har gwamnatin Najeriyar bata yi Adalci akan Sheik Sani Khalifa zariya ba da Hukumomin sojin Kasar Ke ci gaba da tsare shi.
Tun a cikin watan Disambar Bara ne dai aka kama shehin Malamin bisa zargin Yana da alaka da sojojin da ake zargi da yunkurin juyin Mulki a Kasar.
Faruk Yusuf Balaraba shine Shugaban Matasan Tijjaniya na Najeriya a Wani taron Manema Labarai a Minna yace Adalci suke bukata a matsayin su na Cikakkun Yan Kasa.
Tini masana Dokokin Kasa a Najeriyar Suka Fara fashin Baki akan Lamarin ci gaba da tsare shehin Malamin, Barista Bara’u Shehu Kagara, lauya Mai zaman Kansa a Najeriya yace, tsare Malamin har na tsawon watanni Uku ya sabawa dokar kasa.
A baya dai Gwamnatin Najeriyar ta musanta Batun juyin Mulkin Amma Daga bisani Sai Hukumomin sojin Kasar sukace sun kama Wasu Sojoji goma sha shida bisa zargin yunkurin kifar da gwamnatin Bola Ahmed Tinumbu da ayanzu haka suma Sojojin ke ci gaba da zama a tsare.
Daga Minna Ga Rahoton Mustapha Nasiru Batsari


