Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • NEDC : Zata Samar Da Cikekken Kulawa Wa ‘Yan Jaridar Da Sukayi Hatsari A Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Trump Zata Kafa Kasuwar Ma’adanai Amurka
  • An Yanke Mishi Hukuncin Kisa Saboda Neman Kudin Aure Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Babban Malamin Musulunci Sheikh Usman Kusfa Zaria Ya Rasu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Harin Da Israela Ta Kai Gaza Yayi Ajalin Mutane 27 Da Yara Uku Labarai

Maikaba Ya Yi Murabus A Matsayinsa Kocin Wikki Tourist FC
Published: February 9, 2026 at 10:22 PM | By: Bala Hassan

Abdu Mai Kaba Ya Ajiye Aikin Horas da Wikki Tourist fc Bauchi da ke Arewa maso gabas a Najeriya.

Bayan da ƙungiyar kwallon kafa ta Wikki Tourist fc Bauchi ta tashe canjaras da Katsina United 4-4 a wasan mako na 25 cikin gasar Firimiyar lig na Najeriya 25/26.

Ƙungiyar ta shiga rudani bisa irin maki da ta ke zubarwa a gida Wikki Tourist tayi canjaras a wasannin gida har guda 7 an shata a wasa daya a kakar wasan bana, jimillan makin da tayi a sara a gida 17, wadda hakan ya zamo babban kalu-bale a ƙungiyar kuma tana mataki na 15 da maki 29.

Inda wasu ki zargin maihoras da yanwasa Abdu Maikaba na rashin sanya Yan wasa a lokacin da ya dace, har ya kaima wasu magoya bayan Kulub din sukan fadi bakaken maganganu akan sa a zahiri da kuma shafin sada zumunta (Social media ) .na cin mutumcin sa

Saidai wasu masharhanta na gani cewa babu laifin Maikaba matsalar Wikki matsalace ta cikin gida, domin duk Shugaban da aka sauke yana da magoya baya da zasu tsangwami sabon shugaba suma a bangaren sabon babu shiri da wadda ya samesu a ciki musamman ƙungiyar Magoya baya saboda nan ta ke shima sabon shugaba zai sauke Jagororin magoya baya shima ya nada nasa wannan na daya daga cikin matsalolin Wikki ” inji masharhanta a jihar.

“Kuma anki ayi zaben Shuwagabannin magoya baya kamar yadda doka ya tanardar sai dai a bada rokon kwarya.

A gefe guda kuwa masu ruwa da tsaki akan harakar kwallon kafa a jihar wadda dasu aka kirkiri ƙungiyar sun daura laifine akan yadda aka sauka daga tsari da dokokin da aka kafa ƙungiyar.

Abdu Maikaba shi ya dawo da ƙungiyar kwallon kafa ta Wikki Tourist zuwa buga gasar Firimiyar lig na Najeriya

Abdu Maikaba Ya Ajiya Aikinsa a Wikki Tourist
Ga abunda ya rubuta

 

 

 

 

 

 

 

“Ina so in yi amfani da wannan dama domin sanar da hukumar gudanawar kungiyar Wikki Tourists F.C game da shawarar da na yanke na yin murabus daga matsayina na babban mai horaswa (Technical Adviser) na kungiyar, tun daga 09/02/2026 “inji Maikaba

Wannan shawara ta zama dole ne sakamakon dalilai kamar haka:

Rashin hadin kai:
Akwai rashin jituwa tsakanin masu ruwa da tsaki na kungiyar, wanda hakan ke sanya wahalar cimma manyan burin na kungiyar da ta sanya a gaba.

Saboda tsaron lafiya na ina fuskanci
barazanar a yayin gudanar da aikina daga wasu bangarorin magoya bayan kungiyar, bisa yadda suke mun a fili da kuma ta kafafen sada zumunta inji shi.

Saboda wadannan dalilai, na ga ya dace in dauki matakin ajiye aiki bayan na nemi shawarar iyalina.

Ina kuma amfani da wannan dama domin gode wa hukumar gudanawar kungiyar bisa damar da suka bani nayin aiki a wannan babban kulob. Ina fatan za a karbi murabus dina.

 

Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Post navigation

Previous Post: Kasashen Daular Larabawa Tare Da Saudiya Da Jordan Sunyi Allah Wadai Da kasar Israel
Next Post: Yawan Mai Da Kasashen OPEC Suke Hakawo Yayi Kasa Sosai

Karin Labarai Masu Alaka

Shugaba Tinubu Ya Rantsar Da Christ Musa Ministan Tsaro Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Tabbas Atiku Abubakar Ya Karbi Katin Jam’iyyar ADC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Kwankwaso: Gwamnatin Kano Tamuce Baki Daya, Tafiya APC Allah Ya Raka Taki Gona! Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Fadar Shugaban Ƙasan Najeriya Ta Musanta Wani Labarin ƙarya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Amurka Ta Kai Hari Kan ‘Yan ISISI A Jihar Sakkwato Bisa Rokon Gwamnatin Najeriya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Amurka Ta Sanya Hanu Kan Yarjejeniyar Kiwon Lafiya Da Ƙasashen Madagascar, Saliyo, Botswana, Ethiopia Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Muna Kokarin Kawo Karshen Cin Zarafin Jinsi A Gombe – Uwargidan Gwamna
  • Majalisar Dattawar Najeriya Ta Amince Da Tura Sakamakon Zabe Ta Intanet
  • Yeriman Ingila Ya Gana Da Yeriman Saudiya Mai Jiran Gado
  • Dubban Mutane Sunyi Zanga-Zanga A Kasar Australia
  • Bangladesh Tasamu Rangwamen Harajin Da Amurka Ta Kakaba Mata

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Sojoji Sun Yi Juyin Mulki A Guinea Bissau Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Babangida: Hakika Abiola Ya Lashe Zaben Watan Yuni 1993 Labarai
  • Messi Da Cristiano Suna Da Tasiri A Gasar Cin Kofin Duniya 2026 Wasanni
  • Wasu Lauyoyi Sunyi Murabus Yayin Gudanar Da Wata Shari’a A Kasar Amurka Amurka
  • EFCC Ta Cafke Fitacciyar Jarumar Kannywood Samha Inuwa Labarai
  • Shirin Safe 0500 UTC Yau Asabar 11.15.2025 Rediyo
  • Matatar Man Dangote Zata Wadatar Da Najeriya Da Makota Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Kakakin Majalisar Kasar Amurka Yana Tsaka Mai Wuya Game Da Kasafin Kudi Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.