Mataimakin Shugaban Ƙasar Najeriya, Kashim Shettima, ya ziyarci jihar Kwara bayan wani mummunan hari da aka kai ƙauyen Woro wanda ya yi sanadin mutuwar mutane fiye da 75.
Ziyarar ta biyo bayan umarnin Shugaba Bola Ahmed Tinubu, wanda ya yi Allah wadai da harin tare da bayar da umarnin ɗaukar matakan tsaro na gaggawa domin dawo da zaman lafiya.
Shettima ya gana da Gwamna AbdulRahman AbdulRazaq, shugabannin tsaro da na gargajiya, inda ya tabbatar wa iyalan mamatan cewa za a kamo masu aikata laifin a hukunta su.
Ya kuma ce jami’an tsaro sun fara ayyukan leƙen asiri, tare da alkawarin tallafin jin ƙai ga waɗanda abin ya shafa.
Gwamna AbdulRazaq ya gode wa Gwamnatin Tarayya bisa saurin ɗaukar mataki, yayin da shugabannin al’umma suka nemi a ci gaba da tsaurara tsaro domin hana sake aukuwar irin wannan hari.


