Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maikaba Ya Yi Murabus A Matsayinsa Kocin Wikki Tourist FC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • NEDC : Zata Samar Da Cikekken Kulawa Wa ‘Yan Jaridar Da Sukayi Hatsari A Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Trump Zata Kafa Kasuwar Ma’adanai Amurka
  • An Yanke Mishi Hukuncin Kisa Saboda Neman Kudin Aure Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Babban Malamin Musulunci Sheikh Usman Kusfa Zaria Ya Rasu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Muna Kokarin Kawo Karshen Cin Zarafin Jinsi A Gombe – Uwargidan Gwamna
Published: February 10, 2026 at 7:43 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Uwargidan Gwamnan jihar Gombe, Hajiya Dakta Asma’u Inuwa Yahaya,ta jagoranci wani muhimmin taron wayar da kai da nufin ƙarfafa matakan dakilewa da kuma sauya ɗabi’un zamantakewa domin kawo ƙarshen cin zarafin mata da ‘yan mata.

An gudanar da taron ne a Cibiyar Ilimi wato (Education Resource Centre) da ke Tashan Dukku a birnin Gombe, tare da halartar jami’an gwamnati, shugabannin al’umma da na addini, ƙungiyoyin fararen hula, ƙungiyoyin mata, da kuma abokan hulɗar ci gaba.

Shirin, wanda aka aiwatar tare da haɗin gwiwar Ƙungiyar Matan Gwamnonin Nijeriya da kuma tallafin gidauniyar Ford Foundation, ya gudana ne ƙarƙashin taken: “Wayar da Kai don Rigakafi: Sauya Ka’idojin Zamantakewa da Ƙarfafa Ƙudurin Jiha Don Kawar da Cin Zarafin Mata.”

A jawabinta, Hajiya Dakta Asma’u Inuwa Yahaya Wacce Kwamishinar Ma’aikatar harkokin Mata Asma’u Mohammed Iganus ta wakilta ta jaddada cewa rigakafi shi ne hanya mafi tasiri wajen magance matsalar cin zarafi sannan ta bayyana cewa sauya tunani da halayen da ke goyon bayan danniya da take hakkin mata na da muhimmanci wajen gina al’umma mai adalci da mutunta juna.

Uwargidan Gwamnan ta kuma tabbatar da ƙudurin gwamnatin Jihar Gombe na ci gaba da aiwatar da manufofi da shirye-shiryen da za su kare haƙƙin mata da ‘yan mata, tare da samar da ingantattun hanyoyin kai ƙorafi da tallafa wa waɗanda abin ya shafa.

Masu ruwa da tsaki da suka halarci taron sun yi kira ga haɗin kai tsakanin gwamnati, al’umma da ƙungiyoyin fararen hula domin tabbatar da cewa an kawo ƙarshen cin zarafin mata a kowane mataki. Sun kuma yabawa gwamnatin jihar bisa matakan da take ɗauka wajen ƙarfafa tsarin kariya da inganta walwalar mata da yara.

Taron ya kasance wani muhimmin mataki na ƙara wayar da kai da kuma gina aniyar haɗin gwiwa domin samar da al’umma mai zaman lafiya, adalci da mutunta haƙƙin bil’adama.

Labarai, Najeriya

Post navigation

Previous Post: Majalisar Dattawar Najeriya Ta Amince Da Tura Sakamakon Zabe Ta Intanet

Karin Labarai Masu Alaka

Babangida: Hakika Abiola Ya Lashe Zaben Watan Yuni 1993 Labarai
Gwamnatin Tarayya Tana Neman Kudi Domin Aiwatar Da Kasafin Kudin 2026 Najeriya
Tawagar Shirya Gasar Kwallon Sarakuna A Gombe Ta Ziyarci Masarautun Jihar Labarai
Kasashen Thailand Da Cambodia Sun Amince Da Tsagaita Wuta Labarai
An Kashe Mutane 7 A Unguwar Dorayi Dake Kano Najeriya
Kasar China Ta Daina Bada Bashi Da Dalar Amurka Sai Da Kudin Kasar Yuan Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Muna Kokarin Kawo Karshen Cin Zarafin Jinsi A Gombe – Uwargidan Gwamna
  • Majalisar Dattawar Najeriya Ta Amince Da Tura Sakamakon Zabe Ta Intanet
  • Yeriman Ingila Ya Gana Da Yeriman Saudiya Mai Jiran Gado
  • Dubban Mutane Sunyi Zanga-Zanga A Kasar Australia
  • Bangladesh Tasamu Rangwamen Harajin Da Amurka Ta Kakaba Mata

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Gwamnatin Kano: Zamu Kara Daukar Malamai Domin Inganta Ilimi Najeriya
  • Ana Cigaba Da Bincike Game Da Mutuwar Matar Da Likita Ya Manta Almakashi A Cikinta A Kano Najeriya
  • Shugaban Ƙasar China Zai Karbi Bakwancin Shugaban Koriya Ta Kudu Afrika
  • An Gano Wani Kurkukun Sirri Da Ake Azaftar Da Mutane A Kasar Libya Afrika
  • Jami’an Shige Da Ficen Amurka Sun Harbe Wani Har Lahira Amurka
  • Kasar Ukraine Tayi Watsi Da Shiga Kungiyar NATO Labarai
  • An Kai Hari Kan Masu Hakar Ma’adanai A Kasar Mali Tsaro
  • Ana Zargin Wani Dan Kasar Libya Da Fataucin Mutane Tsaro
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.