Rikicin Gabas ta Tsakiya wani Mizani ne da yake nunawa kasashen gabas ta tsakiya cewar Najeriya abokiyar su ce ta cigaba ba a matsayin abokiyar gaba, ko kishiya ba, don taimakawa wajen samar da kayayyaki a lokutan rikici, in ji ministan harkokin wajen kasar Yusuf Tuggar wanda ya shaida wa kamfanin dillancin labarai na Reuters.
Kalaman na zuwa ne a daidai lokacin da yaki a Iran ya kawo cikas ga jigilar kayayyaki ta mashigin Hormuz, hanyar da ta kai kusan kashi biyar na kayan abinci a duniya, lamarin da ya tilastawa masu fitar da kayayyaki zuwa kasashen waje dakatar da jigilar kayayyaki tare da janyo tashin farashin kayayyaki.
Tuggar ya kara da cewar, asusun ajiyar da ba a yi amfani da shi ba a Najeriya yana baiwa kasashen yankin Gulf damar samun wata hanyar samun danyen mai da iskar gas a daidai lokacin da magudanar ruwa a duniya ke da rauni da kuma bukatar samar da iskar gas za ta yi karfi na tsawon shekaru.


