Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Amurka Tayi Barazanar Zata Rage Tallafin Da Take BayarwaSudan Ta Kudu, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Farashin Mai Ya Fadi Fiye Da Dala Daya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Sojojin Najeriya Sun Kashe Fitaccen ’Yan Bindiga Kallamu A Jihar Sakkwato Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya Da Kasar Saudiya Sun Kulla Yarjejeniyar Tsaro Labarai
  • Gwamna Fubara Ya Koma Jam’iyar APC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

RSF Ta Kasar Sudan, Tana Yin Garkuwa Da Mazauna A Yankin Darfur
Published: December 3, 2025 at 8:21 PM | By: Bala Hassan | Updated: December 3, 2025

Shaidun gani da ido, da ma’aikatan agaji da kuma kwararru sun yi zargin cewa rundunar sojojin wucin gadi ta RSF ta kasar Sudan, tana yin garkuwa da mazauna wuraren da ta kama a yankin Darfur tana neman sai ‘yan’uwansu sun biya diyya kafin ta sake su.

Shaidun suka ce wadanda suka kasa biya, ana kashe su, ko a lakkada musu mummunar duka.

Babu tabbas na yawan mutanen da rundunar ta RSF take rike da su a bayan da ta kama al-Fasher, babban birnin Darfur ta Arewa a karshen watan Oktoba, amma an ce ana tsare da su a wurare dabam-dabam a sansanoni da kauyuka da dama dake yanki mai fadin kilomita 80 daga birnin, yayin da wasu ma an maida su cikin al-Fasher ana neman dubban daloli daga hannun ‘yan’uwansu.

Wadanda suka tsira da yawa da suka yi hira da Reuters sun ce ana tilasta ma ‘yan’uwanssu biyan abinda ya kama daga Fam miliyan 5 zuwa fam miliyan 60 na kudin kasar Sudan, kimanin Naira miliyan biyu zuwa miliyan 25 a kudin Najeriya, kafin a sake su, wanda kudi ne mai tsananin yawa a wannan kasa mai fama da talauci.

Wasu shaidu su 11 sun ce wadanda suka kasa biya, ana tattara su a bindige, ko a yi musu mummunar duka. Wani da ya iya samu ya biya ya kubutar da kansa, Mohammed Isma’ila, ya ce ana ba mutum kwana uku ko hudu, idan har ba a aika musu da kudin ba, sai su kashe mutum.

Yace shi da wani dan’uwansa sun tsere daga al_Fasher, amma dakarun RSF suka kama su a wani kauye kuma kowannensu sai da ya biya fam miliyan 10 na kudin Sudan, kimanin Naira miliyan hurhudu, kafin aka sake su.

Da aka nemi jin ta bakinsa, mai ba rundunar RSF shawara kan harkokin shari’a, Mohammed Mukhtar yace, wata kungiya mai adawa da tasu ce da take shigar burtu a matsayin RSF take gudanar da akasarin wannan aiki na kama mutane don neman kudin fansa a ciki da wajen birnin al-Fasher.

Afrika

Post navigation

Previous Post: Guterres: Babban Kuskure Ne Yadda Isra’ila Ta Kai Farmaki A Gaza
Next Post: Hamas Ta Mika Ma Isra’ila Gawar Daya Daga Cikin Mutane Biyu

Karin Labarai Masu Alaka

ECOWAS Zata Taimakawa Kasar Benin Da Dakarun Soji Afrika
ECOWAS Da AU Sun Nuna Damuwa Kan Juyin Mulki A Guinea-Bissau Afrika
Burkina Faso: Mun Kama Sojojin Najeriya da Jirgin Yaki Bisa Shigowa Ba Bisa Ka’ida Ba Afrika
ECOWAS Ta Saka Dokar Ta Baci A Afrika Ta Yamma Afrika
Amurka Na Shirin Kauracewa Taron Kungiyar Kasashen G20 Afrika
Jiragen Saman Yakin Najeriya Suka Gurgunta Yunkurin Juyin Mulki A Benin Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Ministan Tsaro Ya Umarci Janye Sojoji Daga Shingayen Bincike a Tituna
  • Atiku Ya Zargi Gwamnati Da Kama ‘Yan Adawa
  • Rashin Tsaro: Gwamnati Ta Bada Umarnin Daukar Ma’aikata Sama Da 94,000
  • Najeriya Ta Gabatar Da Tayin Karbar Bakuncin Wasannin Afirka Na 2031.
  • Mulkin Kama Karya Yazo Karshe a Kasar Bulgaria

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Rediyo
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • GTA Hausa Logo
    Shirin Dare 2030 UTC Yau Juma’a 11.21.2025 Rediyo
  • An Kai Hari Da Jirgi Mara Matuki A Kusa Da Matatar Mai Din Kasar Sundan Afrika
  • NNPC Da Wasu Kamfanoni Sunyi Yarjejeniyar Iskar Gas Najeriya
  • Trump: Zamu Kawo Zaman Lafiya A Fadin Duniya Amurka
  • Amurka Ta Kama Wani Jirgin Dakon Mai Amurka
  • Shirin Dare 2030 UTC Yau Juma’a 11.21.2025 Rediyo
  • Gwamna Bala Kauran Bauchi Yace Yana Nan Daram a Jam’iyar PDP Siyasa
  • Rashin Tsaro: Gwamnati Ta Bada Umarnin Daukar Ma’aikata Sama Da 94,000 Najeriya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.