Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Sanatan Nasarawa Ta Arewa Ya Rasu A Kasar India
Published: January 2, 2026 at 12:54 PM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: January 2, 2026

Sanata Godiya Akwashiki, mai wakiltar Nasarawa ta Arewa, ya rasu yana da shekaru 52 a wani asibiti da ke ƙasar Indiya.

Rahotanni sun ce ya dade yana fama da rashin lafiya, kuma yana karɓar magani a Indiya kafin rasuwarsa.

Marigayi Akwashiki, wanda aka haife shi a ranar 3 ga Agusta, 1973, a Angba Iggah da ke ƙaramar hukumar Nasarawa Eggon, ya taɓa rike mukamin shugaban masu rinjaye da mataimakin kakakin majalisar dokokin jihar Nasarawa, kafin daga bisani ya zama Sanata a shekarar 2019 karkashin jam’iyyar APC kuma an sake zaɓensa a 2023 karkashin jam’iyyar SDP.

Wani babban mataimaki ga marigayin Sanata, Ajegena Likita Ibrahim, ya tabbatar da rasuwar inda ya bayyana mutuwarsa a matsayin “babban rashi”.

Ibrahim ya shaida wa Daily Trust cewa suna ci gaba da tuntuba da ‘yan uwa a Indiya, amma har yanzu ba a fara shirye-shiryen dawo da gawar Sanata Akwashiki zuwa Najeriya domin jana’iza ba.

Najeriya

Post navigation

Previous Post: Kotu Ta Bada Belin Kwamishinan Kudin Jihar Bauchi
Next Post: Gwamnan Jihar Filato Ya Karbi Katin APC

Karin Labarai Masu Alaka

Take Hakkin Dan Adam Zai Haifar Da Juyin Juya Hali A Najeriya Najeriya
Hukumar NDLEA Ta Kama Wata Mata Da cikin Bogi Na ƙwaya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Gwamnatin Amurka Da Najeriya Sunyi Hadakar Inganta Asibiticin Kiristoci Amurka
Lauya Bala: Tabbas Kotu Zata Soke Zaben Shugaban PDP, Turaki Najeriya
CAN: Da Alamu Daliban St. Mery Na Cikin Koshin Lafiya Najeriya
‘Yan Bindiga Sun Kashe Fiye Da Mutane 50 Tare Da Sace Mata Da Yara A Jihar Zamfara Najeriya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ‘Yan Uwa Musulmi A Jihar Gombe Sunyi Allah Wadai Da Kisan Ayatollah Khomeini
  • An Samu Kaburbura Biyu Dauke Da Gawarwaki 173 A Kasar Kwango
  • Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi
  • Karancin Iskar Gas Kalubale Ne Ga Wutar Lantarki
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Mutane Da Dama Sun Rasa Rayukansu Yayin Rikici A Uganda Siyasa
  • Ana Cigaba Da Kai Kayan Agaji Kasar Morocco Sakamakon Tsananin Hunturu Afrika
  • Wasan Dambe Ya Dau Sabon Salo A Jihar Inugu Wasanni
  • Anakan Bincike Wajen Gano Dan Bindigar Da Ya Kashe Dalibai Biyu A Jihar Rhode Island Amurka
  • Kasar Habasha Da Turkiyya Sun Kulla Yarjejeniyar Makamashi Afrika
  • Ana Tuhumar Dan Shugaba Robert Magabe Da Kisan Kai Afrika
  • Shirin Manuniya Yau Juma’a 12.12.2026 Shirye-Shirye
  • Kotu Ta Bada Belin Kwamishinan Kudin Jihar Bauchi Najeriya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.