Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Najeriya Ta Mika Koke Ga FIFA Tana Zargin DR Congo Ta Sanya ‘Yan Wasan Da Basu Cancantaba Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Tawayen M23 Masu Samun Goyon Bayan Rwanda Basu Jamye A Ulvira Ba Labarai
  • Afirka Ta Kudu Ta Kama ‘Yan ƙasar Kenya Su Bakwai Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Sun Kama Akalla Mutane 13 A Wani Coci A Jihar Kogi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ahmed Musa, Yayi Ritaya A ƙwallon ƙasa Da ƙasa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

SERVICOM, ATBUTH Ta Cafke Wani Da Ake Zargin Dan Damfara Ne
Published: December 17, 2025 at 7:21 PM | By: Bala Hassan

An kama wani Mutum da ake zargi ɗan damfara ne da yake zaluntar masu jinya a Asibiti ATBUTH Bauchi 

Wata takarda da aka rabawa manema labarai ya tabbatar da cewa sashen SERVICOM na Asibitin Koyarwa na Jami’ar Abubakar Tafawa Balewa da ke tarayyar Najeriya a jihar Bauchi, ya danke wani mani Mutum da ake zargin ɗan damfara ne da yake damfarar wadda suka zo jinya a asibitin da danginsu a cikin haraba.

Bayanan na cewar an kama mutumin ne a lokacin wani aikin surru da akayi cikin dare kamar yadda aka saba yi a wasu lokuta, inda aka same wadda ake zargin ya karbi naira dubu 45, daga dangin wani majinyaci da yake samun kulawa sakamakon raunin harbin bindiga.

 

 

 

 

 

 

 

A cewar sanarwar  dauke da sahanun Jami’in Hulda da Jama’a na ATBUTH, Usman Abdullahi Koli tace wanda ake zargin ya nemi a bashi Naira 5,000, a matsayin kuɗin katin asibiti sai kuma Naira 40,000, don sayan magunguna.

Koli, yace ainihin kudin katin asibitin Naira 1,000, ne yayin da kuɗin magungunan suka kai Naira 18,150.

Sai dai an karɓi sauran Naira 27,000 daga hannun wanda ake zargin, inda daga bisani aka mika shi ga hukumar ‘yan sanda don cigaba da bincike da kuma gurfanar da shi a gaban shari’a.

Da yake tsokaci dangane da wannan faruwar wannan lamarin, Shugaban asibitin ATBUTH, Farfesa Yusuf Jibrin Bara, ya yaba wa tawagar ta SERVICOM bisa kokarin su na gano wannan mumunar barnan da kuma sanya ido da suka yi, daga bisani ya sake nanata manufar hukumar asibitin na yaƙi da cin hanci da zamba, kutse a aikin jami’a, da sauran munanan ayyuka.

Inda ya bukaci marasa lafiya da jama’a da su kasance masu lura da al’uman da zasu zo musu da niyar zasu taimakesu, da su gaggauta kai rahoton duk mutanen da basu yarda da shi ba, ko kuma bukatar biyan kudi ba bisa ka’ida ba zuwa ofishin SERVICOM ko su nemi hukumomin asibiti.

Farfesa Bara ya ce yana mai tabbatar da cewa hukumar gudanarwa za ta ci gaba da karfafa hanyoyin sa ido don kare majinyanta da tabbatar da gaskiya a asibitin.

Labarai

Post navigation

Previous Post: Shugaba Tinubu ya mika sunayen Sabbin Shugabannin NMDPRA da NUPRC Bayan Murabus Din Farouk Ahmad Da Gbenga Komolafe
Next Post: Ingila, Hauhawar Farashi Yayi ƙasa Sosai

Karin Labarai Masu Alaka

Ingila, Hauhawar Farashi Yayi ƙasa Sosai Labarai
Fintiri: Zamu Maida Jihar Adamawa Sabuwar Duniya Labarai
Hukumar NAPTIP Ta Kubutar Da Yara 11 Daga Hannun Masu Safara Mutane Labarai
Baba Buhari Yayi Zargin Ansaka Masa Na’urar Tsaro Labarai
Addini Ko Kabilanci Basu Da Gurbi Cikin Ta’addanci Labarai
Gwamnan Jihar Gombe Ya Umurci A Rufe Makarantu Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Fintiri: Zamu Maida Jihar Adamawa Sabuwar Duniya
  • Gwamnatin Najeriya Ta Dauki Matakai Don Farfaɗo Da Maɗaba’ar Gwamnati
  • Boko Haram Sun Dauke Kansiloli A Borno
  • A Kowacce Rana Kasar China Tana Sayan Danyen Mai Ganga Dubu 600 Daga Kasar Venezuela
  • Kotun Kasar Rasha Ta Daure Dan Kasar Belarus Shekarar 22 A Kurkuku

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Fiye Da Mutane 15 A Kasar Australiya Labarai
  • Arteta, Arsenal Zata Yi Sauye-Sauye A Janairu, Wasanni
  • Rikici Tsakanin NNPC Da Kungiyar Gwamnoni Akan Gibin Kudade Labarai
  • Najeriya: Ba Don Leken Asiri Muka Tura Jirgin Yakin Mu Ba Afrika
  • An Murkushe Wani Yunkurin Juyin Mulki A Jamhuriyar Benin Afrika
  • ‘Yan Tawayen M23 Masu Samun Goyon Bayan Rwanda Basu Jamye A Ulvira Ba Labarai
  • Kasashen Cambvodia Da Thailand Sun Kulla Yarjejeniyar Tsagaita Wuta Tsaro
  • An Sace Masu Ibada A Wata Majami’ar Ecwa A Jihar Kogi Tsaro
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.