Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu da takwaran aikinsa na Jamus Chancellor Friedrich Merz, sun tattauna ta wayar tarho kan batun tsaro, makamashi lantarki, da kuma kayayyakin more rayuwa, kamar yadda ofishin shugaban kasan ya fada a ranar Alhamis.
A maganar da suka yi ranar Laraba, na tsawon minti tara, shugabannin biyu sunyi magana kan sake farfado da aikin samar da wutan lanatarki a Najeriya da ya tsaya, da babban kamfanin kasar Jamus SIEMENS zai yi, haka kuma Najeriya zata sayi jirage masu saukar ungulu wadanda ba sababbi bane daga Jamus.
Shugaba Tinubu ya gayawa Mr. Mertz cewa Najeriya tana bukatar taimako wajen sabunta hanyoyin samarda wutan lantarki a kasar.
Wata yarjejeniyar da Najeriya ta kulla da kamfanin SIEMENS a shekara ta 2019, kamfanin zai sabunta hanyoyin raba wutan lantarki da bankunan Jamus za su dauki nauyin aikin, da zimmar idan aka kamala aikin zai samar da wutan lantarki MegaWatts dubu 7, zuwa 2021, sannan ya karu zuwa megawatt dubu 11 zuwa karshen Shekara ta 2023, sai dai aikin ya fuskanci kalubale daban daban da suka hada da kudi, sharuddan gwamnati da makamantar su.
Shugaba Merz na Jamus ya fadawa shugaba Tinubu cewa kamfanin SIEMENS zai yi aikin, kuma a shirye Bankin Deutsche yake ya samar da kudaden tafiyar da aikin, kamar yadda sanarwa daga ofishin shugaban kasar ya fada.
Najeriya da Jamus suna da huldar difilomasiyya na tsawon shekaru 65.


