Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Najeriya Ta Mika Koke Ga FIFA Tana Zargin DR Congo Ta Sanya ‘Yan Wasan Da Basu Cancantaba Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Tawayen M23 Masu Samun Goyon Bayan Rwanda Basu Jamye A Ulvira Ba Labarai
  • Afirka Ta Kudu Ta Kama ‘Yan ƙasar Kenya Su Bakwai Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Sun Kama Akalla Mutane 13 A Wani Coci A Jihar Kogi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ahmed Musa, Yayi Ritaya A ƙwallon ƙasa Da ƙasa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Shugaba Tinubu Ya Gargadi Gwamnoni Game Da Rike Kudaden Kananan Hukumomi Tare Kuma Da Bada Tabbacin Kafa ‘Yan Sandan Jihohi
Published: December 19, 2025 at 5:37 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Shugaban Najeriya Bola Tinubu a ranar Alhamis ya ƙara jaddada ƙudurin sa na kafa ’yan sandan jihohi, inda ya bayyana cewa ya ba wa Amurka da abokan hulɗan Turai tabbacin cewa zai aiwatar da tsarin ’yan sandan jihohi a Najeriya.

Ya jaddada cewa dole ne a kafa ’yan sandan jihohi “ba tare da ja da baya ba” a matsayin wani muhimmin mataki na inganta tsaron cikin gida da ƙarfafa tsarin mulki a matakin jihohi.

Tinubu ya faɗi hakan ne a taron ƙungiyar manyan jiga-jigan APC karo na 14 da aka gudanar a Cibiyar Taron Fadar Shugaban Ƙasa, Abuja.

A wajen taron, ya kuma dage cewa ’dole ne aiwatar da hukuncin cin gashin kan Kananan hukumomi a aikace, inda ya buƙaci gwamnonin jihohi da su daina riƙe kuɗaɗen da aka ware wa shugabannin ƙananan hukumomi.

Jawaban Shugaban Ƙasa sun zo ne a daidai lokacin da matsalolin tsaro ke ƙaruwa a faɗin ƙasar, tare da sabbin kiraye-kirayen neman kafa’yan sandan Jihohi, da kuma ƙoƙarin aiwatar da hukuncin Kotun Ƙoli kan ’yancin cin gashin kai na ƙananan hukumomi da kuma raba musu kuɗi kai tsaye.

Tinubu ya shawarci shugabannin jam’iyya cewa APC, a matsayin ta na jam’iyya mai rinjaye, dole ne ta nuna jagoranci ta hanyar sasantawa, fahimtar juna da sassauci a matakin ƙasa, yana kuma ƙarfafa gwamnonin jihohi da sauran masu ruwa da tsaki da su ɗauki alhakin abin da ke faruwa a jihohin su da ƙananan hukumomin su.

Ya ce kwanan nan ya tattauna da abokan hulɗa na ƙasashen waje, inda ya tabbatar musu da cewa Najeriya za ta tunkari tsarin ’yan sandan jihohi, yana mai ƙarawa da cewa yana da tabbacin jam’iyyar APC za ta bayar da cikakken goyon baya.

Yakara da cewa,“Na yi doguwar tattaunawa da su abokan hulɗa daga Amurka da Tura kuma na faɗa musu cikin alfahari cewa tabbas za mu zantas da dokar ’yan sandan jihohi domin inganta tsaro.”

Najeriya

Post navigation

Previous Post: Kudi Sunfi Rayuwar Mutum Muhimmanci A Asibitocin Najeriya

Karin Labarai Masu Alaka

Tsohon Minista Ngige Ya Shiga Komar EFCC Najeriya
Ganduje: Mun Janye Shirin Kafa Hisbah Mai Zaman Kanta A Kano Najeriya
Kungiyar Kwadago Ta Shirya Zanga-Zanga A Najeriya Najeriya
Gwamna Abba Kabir Ya Hana Yunkurin Kafa Sabuwar Hisba A Kano Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Sabunta Manhajar Ilimi A Duk Matakai Nasara Ce! Najeriya
Masana: ‘Yancin Kasashen Afrika A Rubuce Yake Ba A Zahirance Ba Najeriya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Shugaba Tinubu Ya Gargadi Gwamnoni Game Da Rike Kudaden Kananan Hukumomi Tare Kuma Da Bada Tabbacin Kafa ‘Yan Sandan Jihohi
  • Kudi Sunfi Rayuwar Mutum Muhimmanci A Asibitocin Najeriya
  • Fintiri: Zamu Maida Jihar Adamawa Sabuwar Duniya
  • Gwamnatin Najeriya Ta Dauki Matakai Don Farfaɗo Da Maɗaba’ar Gwamnati
  • Boko Haram Sun Dauke Kansiloli A Borno

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Tsohon Dan-Takarar Gwamnan PDP A Gombe Ya Shiga ADC Siyasa
  • Bahagon Mancha Ya Buge Bahagon Maitakwasara Da Wasun Su! Nishadi
  • An Kafa Majalisar Kotun Sulhu Ta Kano Labarai
  • Ba Shakka Najeriya Zata Iya Shiga Gasar Harbi Ta Duniya Wasanni
  • Makarantun Allo Zasu Yi Gogayya Da Na Boko Labarai
  • Shugaban Guinea-Bissau Umaro Na Fuskantar Matsin Lamba Afrika
  • Wasu Zakaru Da Suka Samu Karramawar Hukumar CAF Ta Afrika Wasanni
  • Amurka Ta Gabatarwa Sassan Dake Yakar Juna A Sudan da Shirin Tsagaita Wuta Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.