Shugaba Tinubu ya taya Musulmi murnar Sallah, tare da kira zuwa ga kishin ƙasa
Shugaban ƙasar Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya taya al’ummar Musulmi murnar Sallar Ƙaramar Idi (Eid-el-Fitr), tare da kira ga su ƙara jajircewa wajen hidimtawa ƙasa da al’umma baki ɗaya.
A cikin wata sanarwa da mai ba shi shawara kan harkokin yaɗa labarai, Bayo Onanuga, ya fitar a ranar Alhamis, shugaban ya bukaci Musulmi su ci gaba da riƙe darussan watan Ramadan, musamman waɗanda suka shafi tsoron Allah, tausayi da haɗin kai tsakanin al’umma.
Ya ce akwai darussa masu yawa da ya kamata a ɗauka daga Ramadan, musamman a irin wannan lokaci, yana mai jaddada muhimmancin bin kyawawan halaye kamar sadaukarwa, juriya, alheri da jin ƙai har bayan watan azumi.
Shugaban ya kuma buƙaci Musulmi su miƙa taimako ga masu buƙata ba tare da la’akari da addini ba, domin ƙarfafa zumunci da haɗin kai a tsakanin ‘yan ƙasa.
Haka zalika, ya roƙi shugabannin addini su yi amfani da wannan lokaci wajen yi wa ƙasa addu’o’in zaman lafiya da ci gaba.
Sanarwar ta ƙara da cewa gwamnatin za ta ci gaba da ƙoƙarin samar da yanayi mai kyau domin walwalar al’umma.


