Shugaban Amurka Donald Trump ya sanar ranar Lahadin cewa, sojojin Ruwan Amurka da sojojin ruwan kasar Iran, sun yi bata kashin, bayan da suka lalata jiragen yakin Iran guda tara ya zuwa yanzu, tare da “bin sauran.”
Trump ya bayyana hakan ne a wani sako da ya wallafa a shafinsa na sada zumunta a yayin da ma’aikatar tsaron Amurka ta Pentagon ta kara kai hare-haren bama-bamai kan sojojin kasar Iran, inda ta tura jiragen yaki na B-2 na boye bama-bamai daga kasar Amurka domin kai hari da kakkausar makamai masu linzami na Iran da bama-bamai mai nauyin kilo 2,000.
Harin na Amurka ya kuma yi kaca-kaca da hedikwatar sojojin ruwan Iran, inda suka lalata ta, in ji Trump.
Sojojin Iran na ramuwar gayya da daruruwan hare-haren makami mai linzami da jirage marasa matuka, kuma Amurka ta tabbatar da mutuwar jami’an Amurka uku na farko da aka kashe a fadan da aka yi ranar Lahadi. Wasu 5 kuma sun samu munanan raunuka yayin rikicin, in ji rundunar sojin Amurka.


