A yau ne ofishin babban kwamishinan sashen kare hakkin dan adam na Majalisar Dinkin Duniya Volker Turk ya ce rundunar ‘yan tawayen Sudan ta RSF sun aikata zalunci matuka da ya karya dokokin yaki lokacin da suka kwato birnin al-Fashir, da kuma yiwuwar aikata laifi na cin zarafin bil-adama.
Birnin na al-Fashir da ke yankin Dafur ya fada hannun ‘yan tawayen ne a watan Octobar bara bayan da dakarun su suka dade suna kewaye da wajen, abin da ya jawo kisan dubbannan mutane.
A hira da aka yi da fiye da mutane 140 da abun ya shafa a arewacin Sudan da kuma gabashin Chad, Ofishin rajin kare hakki na Majalisar Dinkin Duniya ya bada bayanin cewa fiye da mutane 6000 sun rasa rayukan su a kwanaki ukun farko da dakarun RSF suka far ma al-Fashir.
Volker Turk ya kara jaddada kiran sa ga wadanda ke da ruwa da tsaki su dauki matakan da ya kamata don kawo karshen take dokoki da dakarun dake karkashin su suke yi. Ya kuma bukaci kasashe da ke da tasiri su dauki matakin gaggawa don dakile sake afkuwar irin abin da ya faru a al-Fashir.


