Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maikaba Ya Yi Murabus A Matsayinsa Kocin Wikki Tourist FC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • NEDC : Zata Samar Da Cikekken Kulawa Wa ‘Yan Jaridar Da Sukayi Hatsari A Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Trump Zata Kafa Kasuwar Ma’adanai Amurka
  • An Yanke Mishi Hukuncin Kisa Saboda Neman Kudin Aure Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Babban Malamin Musulunci Sheikh Usman Kusfa Zaria Ya Rasu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Shugaban Kasar Amurka Yakara Hana Wasu Kasashe Shiga Amurka Ciki Harda Nijar
Published: December 17, 2025 at 3:22 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Shugaba Donald Trump na Amurka ya kara wasu kasashe 7 cikin kasashen da gwamnatinsa zata haramta ma ‘yan kasar shiga kasar Amurka, cikinsu har da ‘yan Jamhuriyar Nijar.

Fadar White House ta fada ranar talata cewa, shugaba Trump ya sanya hannu a kan wata takardar sanarwa ta karawa da karfafa jerin kasashen da za a sanya ma al’ummarsu takunkumin shiga Amurka a saboda tabbatar da cewa ba su bincika ko bayar da bayanai ga hukumomin Amurka ta yadda zasu iya kare tsaron kasa daga irin wadannan mutane da zasu shigo kasa daga wadannan wurare.

Wannan matakin na ranar talata, a bayan haramta ma ‘yan Jamhuriyar Nijar shigowa Amurka, zai kuma kara da ‘yan kasashen Burkina Faso, Mali, Sudan ta Kudu, Sham ko Syria, da kuma wadanda suke rike da takardun tafiye-tafiye na hukumar mulkin Falasdinu.

Har ila yau wannan matakin yanzu ya haramta shigowar dukkan ‘yan kasashen Saliyo da Laos, wadanda a baya an takaita shigowarsu ne kawai.

Wannan sabon haramcin zai fara aiki daga ranar 1 ga wata mai zuwa na Janairu.

Sanya kasar Sham cikin jerin kasashen na zuwa ne duk da alkawarin da Trump yayi na cewa zai yi duk bakin kokarinsa na ganin kasar ta samu nasarar shawo kan matsalolinta a bayan tattaunawar da yayi da shugaban kasar, Ahmed al-Sharaa, wanda a can baya kwamanda ne na kungiyar al Qaida wanda Amurka ta taba sa takunkumi a kansa.

Fadar White House ta gabatar da hujjar cewa mutanen kasar Sham da suke shigowa Amurka suna ci gaba da zama har bayan karewar takardun bizar su, tana mai cewa dalilinta na daukar wannan matakin a kan Sham ke nan.

Amurka

Post navigation

Previous Post: Kungiyar Kwadago Ta NLC Ta Gudanar Da Zanga-Zanga Bisa Matsalar Tsaro
Next Post: Ahmed Musa, Yayi Ritaya A ƙwallon ƙasa Da ƙasa

Karin Labarai Masu Alaka

Shugaban Trump: Washington Zatayi Cinikayya Da Indiya Amurka
Ministan Kudin Botswana Yace Akwai Hasashen Cewa Tattalin Arzikin Kasar Zai Ragu Amurka
A Hudubar Kirsimeti Paparoma Leo Ya Jajantawa Al’ummar Falatsinu A Yankin Zirin Gaza Amurka
Wasu Kasashen Turai Zasu Daina Tura Sojinsu Wata Cibiyar Sojojin Amurka Amurka
Anakan Bincike Wajen Gano Dan Bindigar Da Ya Kashe Dalibai Biyu A Jihar Rhode Island Amurka
Sanyi Mai Tsanani Da Dusar Kankara Ya Tsaida Al’amura A Amurka Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Indonesia Zata Kafafa Rundunar Kiyaye Zaman Lafiya A Gaza
  • Shugabannin Kasar Australia Sun Bukaci ‘Yan Kasar Suyi Zanga Zanga Cikin Lumana
  • Shugaban Afrika Ta Kudu Yanuna Goyon Bayan Kawo Karshen Yaki Tsakanin Rasha Da Ukraine
  • Ethiopia Tana Horas Da Dakarun RSF A Wani Sansani
  • Majalisar Dottijan Najeriya Ta Amince Da Tura Sakamakon Zabe Ta Na’ura

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Kasashen Duniya Sunyi Tir Da Hambarar Da Gwamnatin Venezuela Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ga Dukkan Alamu Yaki Tsakanin Rasha Da Ukraine Bai Kare Ba Sauran Duniya
  • Najeriya Ta Mika Koke Ga FIFA Tana Zargin DR Congo Ta Sanya ‘Yan Wasan Da Basu Cancantaba Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Janar Christopher Zai Maye Gurbin Ministan Tsaron Najeriya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Tattalin Arzikin Kasar Botswana Zai Farfado Afrika
  • Kasar Uganda Ta Tsare ‘Yan Jam’iyyun Adawa Dubu Biyu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Shirin Safe 0500 UTC Yau Asabar 11.15.2025 Rediyo
  • Za’a Fuskanci Bala’in Yunwa A Najeriya Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.