Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Shugabannin Kasashen Sahel Sunyi Taro a Mali
Published: December 23, 2025 at 5:35 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Shugabanin kasashen Nijar da Mali da Burkina Faso sun fara gudanar da taron kolin kungiyar AES a wannan litinin 22 ga watan disamban 2025 da nufin tattauna batutuwa da dama da suka shafi yankin da rayuwar al’umomin kasashen 3 masu fama da matsaloli iri daya musamman aika aikar kungiyoyin ta’addanci. wasu ‘yan Nijar suka fara bayyana fatansu kan wannan taro kamar yadda za a ji a wannan rahoto da wakilin GTA Hausa Amurka ke Magana Souley Moumouni Barma ya aiko mana daga Yamai.

Janar Abdourahamane Tiani na Nijar da Keftin Ibrahim Traore na Burkina Faso da Assimi Goita na Mali shugaban rikon kungiyar AES a yayin zaman na wuni biyu za su yi bitar ayyukan hadin guiwar da suka gudanar a kungiyance kafin su tattauna kan batutuwan da zasu fi baiwa fifiko a nan gaba musamman ta inda za su bullowa lamarin tsaro, tattalin arziki aiyukan ci gaban jama’a diflomasiya da dai sauransu. shin ko ya ‘yan Nijar ke kallon wannan taro.?

Koda yake yanayin tsaro na kan gaban abubuwan da aka fi nuna damuwa kansu, ‘yan fafutika irinsu Hamidou Sidi Fody na kungiyar kulawa da Rayuwa na shawartar shugabanin kasashen 3 su kuma kara duba wata matsalar ta daban da ke dabaibaye harakokin tattalin arziki.

Nijar da Mali da Burkina Faso na cikin wata fafutikar tabbatar da ‘yancin kai a yayin da alamu ke nuna bayyanar babban sauyi a tafiyar siyasar duniya ta yau. abin da ke kara wa jama’ar yankin AES kwarin guiwa a game da manufofin da shugabanin kasashen 3 suka sa gaba sai dai akwai abin lura.

kungiyar AES ta samo asali a watan satumban 2023 kafin ta zama gamayya bayan watanni biyu da zumma duba alkibla guda a game da dukkan batutuwan da suka shafi tsaro diflomasiya tattalin arziki da sauransu, kasashen 3 sun fice daga CEDEAO a janerun 2024 saboda zargin kungiyar da zama ‘yar amshin shatan kasashen yammaci. sannan sun kori sojojin Faransa daga yankin sahel. daga bisani sun kafa rundunar hadin guiwa mai dakaru 5000 wace a karshen makon jiya aka kaddamar da aiyukanta a hukumance a ci gaba da jan damarar yaki da kungiyoyin ta’addanci.

Afrika

Post navigation

Previous Post: Kananan Hukumomi Na Kokarin Karbar Kudadensu Daga Jihohi
Next Post: Mayakan M23 Sun Tsagaita Wuta A Gabashin Kwango

Karin Labarai Masu Alaka

ECOWAS Ta Saka Dokar Ta Baci A Afrika Ta Yamma Afrika
Shugaban Mulkin Soja A Mali Ya Kirkiro Mukami Kamar Minista Afrika
Shugabannin Kasashen Afirka Ta Tsakiya Sun Kamallah Taron Koli Afrika
Gwamnatin Sham Tace Harin Kurdawa Ya Hallaka Sojojin Kasar Afrika
Gwamnatin Kasar Nijar Ta Kame Babban Dan Jarida Afrika
Afirka Ta Kudu Ta Samu Rigakafin Cutar Boro Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ‘Yan Uwa Musulmi A Jihar Gombe Sunyi Allah Wadai Da Kisan Ayatollah Khomeini
  • An Samu Kaburbura Biyu Dauke Da Gawarwaki 173 A Kasar Kwango
  • Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi
  • Karancin Iskar Gas Kalubale Ne Ga Wutar Lantarki
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Gwamnatin Najeriya Ta Ayyana Ranakun Hutu Najeriya
  • Gwamnatin Jihar Gombe Ta Haramta Sana’ar Bola Jari Tsaro
  • Shahararren Dan Dambe Anthony Joshua Yayi Hatsarin Mota A Jihar Ogun Labarai
  • Babban Hafsan Sojan Libya Ya Mutu A Wani Hatsarin Jirgin Saman Turkiyya Afrika
  • Gwamnatin Kasar Nijar Ta Kame Babban Dan Jarida Afrika
  • Ana Cigaba Da Samun Hare Hare Da Jiragen Marasa Matuki A Sudan Labarai
  • Amurka Ta Kai Hari Kan ‘Yan ISISI A Jihar Sakkwato Bisa Rokon Gwamnatin Najeriya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Jiragen Saman Yakin Najeriya Suka Gurgunta Yunkurin Juyin Mulki A Benin Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.