Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Najeriya Ta Dauki Hayan Amurkawa Don Kyautata Alaka Da Trump Game Da Kisan Kiristoci Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Tarayya Ta Cimma Yarjejeniya Da Kungiyar Malaman Jami’oi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Amurka Ta Baiwa Najeriya Wasu Muhimman Kayan Yaki Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Trump Yayi Kira Ga ‘Yan Ƙasar Iran Su Ci Gaba Da Zanga Zanga Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Syria: Mutane Sun Yi Zanga Zanga Domin Nuna Rashin Amincewa Da Korar Kurdawa A Birnin Aleppo Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Yau Litinin Ake Cigaba Da Shari’ar Najib Zarak
Published: December 22, 2025 at 9:09 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Ranar litinin tsohon fira ministan kasar Malaysia, Najib Razak, zai san ko zai iya karasa sauran hukuncin daurin da aka yanke masa a gidansa, ko kuma a cikin kurkuku.

An yanke ma Razak hukuncin daurin shekaru 12 a gidan kurkuku a shekarar 2022, bisa laifin zarmiya da cin hanci a badakalar da aka fi sani da sunan abin Fallasa na 1MDB.

A shekarar da ta shige, wata hukumar yahudawa dake karkashin jagorancin tsohon Sarkin Malaysia, ta rage masa hukumcin zuwa shekaru 6.

Amma Razak ya ce Sarkin na Malaysia ya kuma bada umurnin cewa yana iya karasa wannan hukuncin a gidansa, watau daurin talala, kuma abinda ya sa ya shigar da kara ke nan a kotu yana neman a yi aiki da wannan umurnin da gwamnatin fira minista Anwar Ibrahim ta ce ba ta san da shi ba.

Jami’an gwamnati sunyi wata da watanni suna cewa ba su da wata masaniya game da wannan takardar umurni, duk da cewa a cikin wannan shekara, ofishin tsohon sarkin da ma wani lauya na tarayya sun gaskata cewa lallai an bayar da takardar umurnin rege hukumcin zuwa shekaru 6, kuma za a iya kyale ya karasa a gidansa.

Ranar litinin, babbar kotun birnin Kuala Lumpur zata yanke hukumci a kan wannan, kwanaki hudu kafin ta yanke hukunci a kan shari’a mafi girma da shi Najib yake fuskanta dangane da wannan abin fallasa na asusun 1Malaysia Development Berhad, wanda asusu ne na kudin gwamnati da ya taimaka wajen kirkirowa a shekarar 2009.

Masu fashin baki suka ce mutane ba zasu yi murna ba, musamman magoya bayan fira minista Anwar, idan kotun ta wanke shi a wancan zargin, Anwar dai ya ci zabe ne bisa alkawarin yaki da cin hanci da rashawa.

Labarai

Post navigation

Previous Post: Rasha Ta Nuna Kudurin Cimma Zaman Lafiya Da Ukraine
Next Post: Ministocin Kasar Asia Zasu Gudanar Da Taro A Kasar Malaysia

Karin Labarai Masu Alaka

Shin Ko Ganawar Zelensky Da Macron Zata Haifar Da ‘Da Mai Ido? Labarai
Za A Rantsar Da Mainasara Kogo A Matsayin Shugaban Kundin Da’ar Ma’aikata Labarai
Kasashen AES Sun Buɗe Gidan Talabijin Na Bai Daya Afrika
Shahararren Dan Dambe Anthony Joshua Yayi Hatsarin Mota A Jihar Ogun Labarai
Kamfanin Hakar Ma’adanai Na Kasar Kanada Ya Cigaban Da Aikinsa Labarai
Bisa Alamu Hadinkan Kasashen Yankin Sahel Zai Haifar Da Nagarta Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Najeriya Ta Dauki Hayan Amurkawa Don Kyautata Alaka Da Trump Game Da Kisan Kiristoci
  • Gwamnatin Tarayya Ta Cimma Yarjejeniya Da Kungiyar Malaman Jami’oi
  • Kabiru Vice: Najeriya Zata Iya Nasara A Kan Moroko AFCON 2025.
  • Motar Yashi Ta Kashe Mutane Shida A Wani Coci Dake Legas
  • An Kaddamar Da Rijistar Zamani Ta Zamowa Mamba A Jam’iyar APC

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Adamu: “Yakar Cin Hanci Daga Tushe Itace Mafita Daya Tilo” Labarai
  • Cutar Zazzabin Lassa Tayi Ajalin Mutum 1 Yayinda Mutane 11 Suka Kamu A Jihar Gombe Najeriya
  • Gwamna Fubara: Rashin Kariya daga PDP Ne Ya Tilasta Ni Komawa APC Siyasa
  • Najeriya: Ta Aiwatar Da Tsarin Ba Aiki Ba Albashi Ga Ma’aikata Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Matatar Man Dangote Ta Samu Tagomashi Daga Abokan Hulda Najeriya
  • ‘Yan Ta’adda Sun Hallaka Malaman Makaranta A Tilabery Afrika
  • Bola Ahmed Tinubu Ya Soke Bashin Da Gwamnati Take Bin NNPC Najeriya
  • NUJ: Akwai Bukatar Samar Da Inshorar Lafiya Ga ‘Yan Jarida A Najeriya Rediyo
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.