Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Jarman Deba Ya Kada Senata Goje A Zaben Fidda Gwani Afrika
  • Jami’an ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayi Afrika
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai Afrika
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika

Masana: ‘Yancin Kasashen Afrika A Rubuce Yake Ba A Zahirance Ba
Published: December 7, 2025 at 5:16 PM | By: Yusuf Aliyu Harande

Tun fiye da shekaru sittin da mafi yawan kasashen Afirka suka sami ‘yancin kai, masana sun bayyana cewa har yanzu nahiyar na fama da tsarin mulkin mallaka da rashin samun ‘yanci a fannoni daban-daban na rayuwa.
A wani taro da masana daga kasashen duniya suka halarta, da masu fafutukar ‘yanci da hukumomi da dalibai daga kasashe daban-daban na Afirka, wadanda suka taru a Jami’ar Jos, an gabatar da kasidu da suka yi nazari kan makomar Nahiyar Afirka da hanyoyin samar da mafita.
Taron na tunawa da wani matubuci da fafutuka, Frantz Fanon da yayi rubuce-rubuce da suka zame kamar wahayi kan makomar nahiyar Afirka a fannonin damokradiyya, gazawar shugabanci da sauransu.
Malam Jibrin Ibrahim na cibiyar damokradiyya da ci gaba dake Abuja, Najeriya, yace taron yayi nazari ne kan rashin tasiri da ‘yancin kai a Afirka ya kasance.
Shima Malam Yunusa Zakari-Ya’u na cibiyar fasahar sadarwa da ci gaba dake Kano, Najeriya, yace yawan juyin mulki da ake samu a wassu kasahen Afirka, saboda rashin adalcin shugabanni ne.
Komared Sam Magaji, malami a Jami’ar Jos, yace suna horadda dalibai su san yadda shugabanni a baya suka yi mulki, da yadda daliban zasu yi nazarin abubuwan dake faruwa yanzu, da yadda za’a yi gyara nan gaba.
Mr Charles Toheyo, malami a Jami’ar Nkerere dake kasar Uganda, yace idan har shugabannan dake mulki basu sauya tunaninsu ta yadda zasu kyautata wa al’umma ba, to ba shakka za’a ci gaba da zaman tankiya.
Adam Khalid, dalibi a Jami’ar Jos, yace matasa a Afirka a shirye suke su kawo sauyi, sai dai har yanzu basu sami jagoranci daga dattawa ba, saboda dattawan kansu kadai suka sani.
A taron na wuni biyu, an gabatar da kasidu kimanin saba’in, da suka kunshi samarda mafita kan matsalolin da suka hana kasashen Afirka samun walwala da ci gaba.
https://gtahausa.com/wp-content/uploads/2025/12/DAMOKRADIYYA-A-AFIRKA.mp3
Najeriya

Post navigation

Previous Post: Gwamnatin Bauchi: Ba Zamu Bude Makarantu Ba Sai 2026
Next Post: Marc Brys: “Eto’o Baiyi Adalci Ga Onana, Da Vincent, Ba”

Karin Labarai Masu Alaka

Fadar Sarkin Musulmi: Talata Ne 1 Ga Watan Sha’aban Na 1447AH Najeriya
APC Ta Yi Babban Taron Amincewa Da Shugabannin Jam’iyyar Ba Hamayya Najeriya
Suvr Jahun: Ya Kamata Obasanjo Ya Bar Al’umar Ƙasa Su Fito Da Wadda Suke So 2027 Najeriya
Mayakan Boko Haram Da ISWAP Sun Kai Hari Cikin Dare Afrika
An Gudanar da Taron Kwana Biyu kan Tsarin Sa Ido da Tantance Ayyukan AGILE a Jihar Gombe  Afrika
Majalisar Tattalin Arzikin Najeriya Ta Bawa Gwamnan Kebbi Mukamin Kyautata Harkar Kiwo Najeriya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jarman Deba Ya Kada Senata Goje A Zaben Fidda Gwani
  • Jami’an ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayi
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Kasar Chadi Ta Rufe Iyakar Ta Da Kasar Sudan Afrika
  • An Sace Masu Ibada A Wata Majami’ar Ecwa A Jihar Kogi Tsaro
  • Motar Yashi Ta Kashe Mutane Shida A Wani Coci Dake Legas Najeriya
  • Amurka Zata Bawa Ukraine Tsaro Na Musamman Amurka
  • Wani Jami’in Iran Yace Amurka Taso Kanta A Tattaunawar Tsagaita Wuta Amurka
  • Hukumar Zabe A Najeriya Ta Cigaba Da Rijistar Katin Zabe Labarai
  • Rikici Ya Barke A Kano Bayan Kashe Wani Matashi Da Ake Zargi Da Kashe Ladani Najeriya
  • Shugaba Trump Ya Kara Matsin Lamba Kan Iran Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.