Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro Labarai
  • Za A Cigaba Da Tattaunawa Domin Kawo Karshen Yakin Gabas Ta Tsakiya Amurka
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Dangantaka Tayi Tsamari Tsakanin Salah Da Slot.
Published: December 8, 2025 at 7:30 PM | By: Bala Hassan

Dangantaka Tayi Tsamari Tsakanin Salah Da Slot,

Dangantakar ta kara Tsamari ne bayan da Kocin Liverpool, Arne Slot ya cire jeren sunayen tawagar da za ta fafata da Inter Milan, ba tare da Salah ba, bayan dan wasan dan Ƙasar Masar yayi wasu kalamai masu tayar da hankali a kwanaki da suka haifar da rikici a Anfield.

An cire fitaccen dan wasan Liverpool Mohamed Salah daga tawagar da za ta fafata da Inter Milan a gasar zakarun Turai wadda hakan ya tada sabon rikici da kocin Arne Slot.

Tsohon dan wasan a Anfield, wanda ya taka rawar gani wajan samun nasarar Liverpool a gasar Premier a kakar wasa ta bara a karkashin Slot, yanzu yana fuskantar makoma mara tabbas a kulob din hakan na kara ruruwa wutan rikici a bayan fage.

Majiyoyin da ke kusa da ƙungiyar sun bayyana cewa rikicin da ya ɓarke ​​tsakanin Salah da Slot ya wargaza dangantakar da ta daɗe tana tsakanin ɗan wasa da koci bayan wani rahoto daga Fabrizio Romano cewa za a iya cire ɗan wasan na Masar.

Hakan ta biyo bayan maganar da Salah ya yi bayan da aka ajiye shi a benci  karo na uku a jere ciki harda wasan da Liverpool tayi da Leeds United, inda kalaman bai yi wa Slot daɗi ba, wanda hakan ya haifar da rashin jituwa da masu sharhi suka bayyana a matsayin “wanda ba zai iya gyaruwa ba.”

Wannan rashin jituwa ya yi tsanani har aka cire Salah daga tawagar Liverpool da za ta je Italiya don fafatawa da Inter Milan UCL, wanda hakan ke nuna sako a bayyane daga shugabannin ƙungiyar.

Duk da Salah ya atisaye da ‘yan uwansa, magoya bayan Liverpool suna mamakin wannan mataki, ganin yadda Salah ya kasance ɗaya daga cikin manyan ‘yan wasan ƙungiyar da kuma muhimmiyar rawar da ya taka a kakar wasansu ta Zakarun Turai.

Rashin ɗan wasan gaban na Masar ya haifar da manyan tambayoyi game da alkiblar ƙungiyar da kuma yadda suke shirin durkusar da hazakarsa a gaba.

Yayin da wannan labarin ke ci gaba da bayyana, magoya bayan Liverpool suna jira don sanin ko tauraron dan wasansu zai iya murmurewa daga wannan rikicin.

Wasanni

Post navigation

Previous Post: Nuhu Ribadu Ya Mika Dalibai 100 da Aka Ceto Ga Gwamnatin Jihar Neja
Next Post: Shugaba Tinubu: Naji Dadin Sako Daliban Neja Da Aka Sace

Karin Labarai Masu Alaka

Wasu Zakaru Da Suka Samu Karramawar Hukumar CAF Ta Afrika Wasanni
Abu Mafi Daukar Hankali A Wasan Dambe Na Yau Wasanni
Onana Ba Ya Cikin Tawagar Kamaru (AFCON) Wasanni
AFCON ChelIe, Ya Fidda Sunayen ‘Yan Wasan Super Eagles Na Karshe. Wasanni
Anyi Jefe-Jefe Yayin Rangadin Messi, A Indiya Wasanni
FIFA, Ta Tabbatar Da Ranar Mika Sunayen ‘Yan Wasa AFCON 2025. Wasanni

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jami’yar ADC A Najeriya Ta Kori Nafiu Bala
  • ADC Ta Kaucewa INEC Ta Gudanar Da Babban Taro
  • ‘Yan Sanda Sun Kama Mutane 33 Bisa Zargin Kai Hari A Jihar Kwara
  • Papa Roma Leo Yayi Gargadi Game Da Rushewar Dimokraɗiyya
  • Jiragen Ruwa Suna Biyayya Ga Dokar Hana Ketare Ruwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Layin Raba Wutan Lantarki Na Najeriya Ya Fashe Labarai
  • Ministan Tsaro Ya Umarci Janye Sojoji Daga Shingayen Bincike A Tituna Najeriya
  • Najeriya Na ƙoƙarin Shiga Gasar Cin Kofin Duniya 2026 Ta Barauniyar Hanya Wasanni
  • Tabbas Atiku Abubakar Ya Karbi Katin Jam’iyyar ADC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyoyin Premier 17 Za Su Rasa ‘Yan Wasa 40 saboda Gasar AFCON 2025, Wasanni
  • Yakin Gabas Ta Tsakiya Ya Haifar Da Tsadar Taki Da Mai Ga Manoma Labarai
  • Ganduje Ne Yasa Aka Kama Ni Inji Muhuyi Magaji Najeriya
  • Wani Harin ‘Yan Bindiga Ya Kashe Mutane 35 A Jihar Borno Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.