Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Tsohuwar Jarumar Kannywood Wasila Ismail Ta Rasu Afrika
  • Za’a Fassara Hudubar Arfa Da Harshen Hausa Afrika
  • An Kamallah Jigilar Alhazain Najeriya Domin Hajjin 2026 Afrika
  • Bola Ahmed Tinubu Ya Lashe Zaben Fidda Gwani Na Shugaban Kasa A Gombe Afrika
  • APC Ta Ayana Tsohon Gwamnan Bauchi M.A Abubakar A Matsayin Dan Takarar Gwamna Afrika

Gwamnatin Bauchi Ta Amince Domin Inganta Kasuwancin Nama A Jihar
Published: December 11, 2025 at 6:37 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Gwamnatin jihar Bauchi ta amince da fitar da naira miliyan 97 domin sabunta masana’antar sarrafa nama ta jihar da ke Bauchi, a wani bangare na kokarinta na farfado da harkokin kiwo da sarrafa nama a jihar.

Kwamishinan Ma’aikatar kyautata Kiwo, Dr. Musa Lukshi ne ya bayyana hakan yayin wani ziyarar duba ci gaban aikin da ake yi a masana’antar.

Ya ce kudaden da Gwamna Bala Abdulkadir Muhammad ya fitar da gaggawa, alama ce ta kudurin gwamnati na inganta darajar sarkar kiwo da kara tabbatar da inganta abinci da ake samarwa al’umma.

Dr. Lukshi ya ce aikin sabuntawar zai hada da girka kayan aiki na zamani, wanda zai taimaka wajen ingantawa tare da tsaftace tsarin aiki da kuma ingancin nama da ake samarwa.

Ya kara da cewa bayan kammala aikin, masana’antar za ta samar da guraben ayyukan yi ga matasa da sauran ma’aikata, tare da bunkasa tattalin arziki da kudaden shiga ga jihar.

Masu kiwo da sauran masu ruwa da tsaki sun bayyana jin dadinsu da shirin, suna masu fatan zai samar da kasuwa mai dorewa, inganta farashi, da rage asarar da ake fuskanta bayan yanka.

Labarai

Post navigation

Previous Post: Sarkin Musulmi Yayi Magana Game Da Matsalar Tsaron Kasar
Next Post: Amurka Ta Nuna Damuwa Kan Matsalar ‘Yan Gudun Hijira A Najeriya

Karin Labarai Masu Alaka

Shugaban Lebanon Ya Nemi Gudanar Da Shawarwari Kai Tsaye Afrika
Harin Iran A Kasar Saudiya Ya Haifar Da Tattaunawa Tsakanin Shugabanni Afrika
Kawayen Amurka Bazasu Shiga Matakin Shugaba Trump Ba Amurka
Za’a Fuskanci Bala’in Yunwa A Najeriya Labarai
Ana Cigaba Da Tattaunawa Tsakanin Trump Da Zelensky Domin Tsagaita Wuta A Ukraine Labarai
Shugaba Trump Yace Amurka Ce Zata Rika Gudanar Da Harkokin Kasar Venezuela Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Tsohuwar Jarumar Kannywood Wasila Ismail Ta Rasu
  • Za’a Fassara Hudubar Arfa Da Harshen Hausa
  • An Kamallah Jigilar Alhazain Najeriya Domin Hajjin 2026
  • Bola Ahmed Tinubu Ya Lashe Zaben Fidda Gwani Na Shugaban Kasa A Gombe
  • APC Ta Ayana Tsohon Gwamnan Bauchi M.A Abubakar A Matsayin Dan Takarar Gwamna

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Gwamnatin Kano Ta Samar Da Wasu Dabarun Inganta Tsaro Tsaro
  • Rundunar ‘Yan Sanda Sun Ceto Wani Daga Hannun Masu Garkuwa Najeriya
  • Kasar Saudiya Zata Cika Azumi Talatin Kimiya
  • Ruwan Sama Yayi Ajalin Daruruwan Mutane A Afirka Ta Kudu Afrika
  • Afirka Ta Kudu Ta Bayyana Yadda Aka Yaudari ‘Yan Kasar Ake Tilasta Musu Ayyukan Bauta Afrika
  • Shirin Dare 2030 UTC Yau Alhamis 11.20.2025 Rediyo
  • Najeriya Da Kasar Saudiya Sun Kulla Yarjejeniyar Tsaro Labarai
  • CBN: An Samu Ƙaruwar Masu Cin Bashin Banki Basa Biya Najeriya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.