Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

Ministan Yaɗa Labarai: Ceto Daliban Neja An Samu Natsuwa A Kasa
Published: December 11, 2025 at 7:56 AM | By: Bala Hassan | Updated: December 18, 2025

Ceto ɗaliban Neja ya dawo da natsuwa ga ƙasa, inji Ministan Yaɗa Labarai.

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris ya ce ceto ɗaliban da aka sace daga Makarantar Firamare da Sakandare ta St. Mary da ke Papyri, Jihar Neja, ya dawo da natsuwa da kwanciyar hankali ga iyalan su da ƙasa baki ɗaya.

Ministan ya bayyana hakan ne a ranar Laraba lokacin da ya jagoranci tawagar Gwamnatin Tarayya zuwa Fadar Gwamnatin Jihar Neja domin yin godiya da kuma bayyana jin daɗin dawowar yaran lafiya.

 

 

 

 

 

 

Tawagar ta samu tarbar Gwamnan Jihar Neja, Umaru Mohammed Bago.

Idris ya jaddada cewa haɗin kai tsakanin jami’an tsaro, Gwamnatin Jihar Neja da al’ummar yankin ne ya taimaka wajen nasarar aikin ceton.

Ya ce: “Ceton waɗannan yara ya dawo da natsuwa ga iyalan su da kuma ga ƙasa baki ɗaya. Mun yaba da jajircewar jami’an tsaro, saurin ɗaukar matakin Gwamnatin Jihar Neja, da kuma haɗin kan al’umma wanda ya ba da damar samun wannan sakamakon.”

Ministan ya kuma jaddada cewa gwamnatin Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ta ɗauki tsaron makarantu da kare ɗalibai da matuƙar muhimmanci.

Ya ƙara da cewa, “Dole ’ya’yan mu su samu damar yin karatu cikin tsaro. Gwamnatin Tarayya tana da cikakkiyar niyyar ci gaba da aiki tare da jihohi domin ƙarfafa tsaron makarantu, tare da tabbatar da cewa irin wannan ɓarna ga zaman lafiyar mu bai da wurin zama a ƙasar mu.”

A jawabin sa, Gwamna Bago ya gode wa Ministan bisa ziyarar, tare da yaba wa jami’an tsaro da al’ummomin yankin waɗanda suka taka rawa wajen ganin an sako ɗaliban.

Ya kuma jaddada cewa jihar za ta ci gaba da aiki tare da Gwamnatin Tarayya domin ƙarfafa tsaro da zaman lafiya.

Labarai

Post navigation

Previous Post: Amurka Ta Nuna Damuwa Kan Matsalar ‘Yan Gudun Hijira A Najeriya
Next Post: Gwamnatin Tarayya Tana Neman Kudi Domin Aiwatar Da Kasafin Kudin 2026

Karin Labarai Masu Alaka

Sojin Najeriya Da Amurka Sun Hallaka Jagoran ISIS Afrika
Hukumomin Tsaron Kenya Sunce ‘Yan Kasar Suna Fafata Yaki Da Dakarun Rasha A Ukraine Afrika
Gwannatin Jihar Kebbi Ta Arawa Maniyyata Kuɗin Aikin Hajji 2026, Labarai
Gwamnatin Amurka Na Kokarin Watsi Da Tsohuwar Dokar Jones Labarai
Shugaba Tinubu: Naji Dadin Sako Daliban Neja Da Aka Sace Labarai
Gwamnatin Gombe Ta Aza Tubalin Gina Sakatariyar Gundumomin Cigaba (LCDAs) Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Hukumar NDLEA Ta Kama Wata Mata Da cikin Bogi Na ƙwaya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Hukumar ‘Yan Sanda Ta Bukaci Jama’ar Jos Ta Arewa Su Rika Bin Doka Afrika
  • Isra’ila Takai Sabon Hari Tehran Ranar Lahadi Labarai
  • MDD: Fiye Da Farar Hula Metan 200 Suka Mutu A Sudan Afrika
  • Ethiopia Tana Horas Da Dakarun RSF A Wani Sansani Afrika
  • Masu Ruwa da Tsaki akan Lamurran Siyasa sun Fara Maida Martani akan Matakin da Ministan Labaran Nigeria da wayar da kan Jama,a Idris Malagi na korar Daya Daga cikin Ma,aikatansa Saboda dalilai na Siyasa. da tsakiayar ranar Wannan larabace dai Mataimakin na Musamman akan yada Labarai ga Minista Malagi Malam Rani,u Ibrahim ya fitar da Wata sanarwar cewa Ministan ya Dakatar da Daya Daga cikin Ma,aikatansa Mai Suna Sa,idu Enagi Saboda ya fitar da Wani bayani a Kafar yada Labarai na sada zumunta dake Nuna Ministan ya shirya tsaf Domin takarar Gwamnan Jihar Neja a 2027. Malam Sa,idu Etsu Tsohon Dantakarar Shugaban cin Jam,iyyar APC a Nigeria Yace Matakin da Ministan ya Dauka yayi Dai dai Domin yanzu lokaci baiyi ba..ceu.. Shima Dattijon Siyasa a Jihar Neja Alh.Awaisu Giwa Kuta Yace Matakin da Ministan Labaran ya Dauka yayi Dai dai Domin yanzu Jihar Neja zaman Makoki Ake na fotinar Yan ta,adda ba wai Batun Neman Mukamin Siyasa ba..ceu .in.. To Sai jigon Jam,iyyar PDP Mai Adawa a Nigeria Hon.Yahaya Ability Yace Akwai kuskure Babba da Ministan ya tabka a dai dai Wannan Zamani na Siyasa duk da cewa Jihar Nejan na cikin Yanayi na masifar Yanbindiga..ceu..in .. Azaben Shekara ta 2023 Malagi ya kara yayi Takara Gwamnan Jihar Neja a jam,iyyar APC inda Gwamna Umar Bago ya kadashi a zaben fidda Gwani.
    Martanin Wasu ‘Yan Najeriya Ga Ministan Labarai Bisa Korar Dadiminsa Najeriya
  • Sojojin Da Suka Kifar Da Farar Hula A Guinea-Bissau Sun Sanar Da Cewa! Afrika
  • Mayakan RSF A Sudan Suna Sace Kananan Yara A Lokacin Yake-Yaken Kasar Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.