Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Makarantun Allo Zasu Yi Gogayya Da Na Boko
Published: December 12, 2025 at 9:43 PM | By: Bala Hassan | Updated: December 13, 2025

Nan bada jimawa ba Makarantun Allo zasu yi gogayya da takwarorinsu na Boko dake faɗin Kasa. ”in ji Minitan Ilimi na Tarayyar Najeriya.

Ministan Ilimin Najeriya Dakta Tunji Alausa yace tsarin ingatawa tare da koyar da Karatun Allo da ilimin Tsangayu dake da manufar inganta karatu da rayuwar Almajirai da aka kaddamar ranar Litinin din data gabata, manufar samar da tsarin bai daya da za a rinka amfani da shi a matakin kasa baki daya.

 

 

 

 

 

 

Da yake karin haske dangane da wannan gagarumin sauyi da ma’aikatar ilimin ke kokarin aiwatarwa, maitaimakawa Ministan ilimin Najeriya kan ilimin Almajirai da Tsangayu hadi da makarantun Allo, Dr. Balarabe Shehu Kakale, Barden Tsangayu da Makarantun Allo na Kasar Hausa yace nan bada jimawa ba Makarantun Allo zasu yi gogayya da takwaroinsu na Boko dake faɗin kasar.

Haka zalika, Dr. Kakale, ya kara da cewa kafin akai ga wannan matsayar, sai da suka karade daukacin shiyyoyin siyasa shida na Najeriya inda suka tattauna da masu ruwa da tsaki da suka hada da Malamai da sarakuna da Kungiyar kiristoci ta Najeriya wato CAN, sai dai ya bayyana bukatar dake akwai wajen ganin gwamnatocin jihohi sun kara damba domin kaiwa ga cikakkiyar Nasara.

Tun da fari, Dr. Balarabe Shehu Kakale tsohon danmajalisar tarayya Najeriya, ya yabawa Ministan ilimin Najeriya Dakta Tunji Alausa da Ministan kasa a ma’aikatar ilimin kasar Dr. Suwaiba Ahmed da kuma shugaban hukumar kula da ilimin Almajirai da yara da basa zuwa makaranta ta kasar Dr. Mohammed Sani Idris hadi da jagororin addinai da sarakuna bisa matakan da suke dauka na inganta ilimin Almajirai dama rayuwar yaran da basa zuwa makaranta ta hanyar koyar da su sa’o’in hannu da zai basu damar dogaro da kan su.

Labarai

Post navigation

Previous Post: Amurka Na Gargadin Rwanda Da Ta Mutunta Alkawali
Next Post: Kasashen Cambvodia Da Thailand Sun Kulla Yarjejeniyar Tsagaita Wuta

Karin Labarai Masu Alaka

An Gudanar Da Addu’o’i Na Musamman Don Neman Zaman Lafiya Labarai
Gwamna Ahmad Aliyu Na Jihar Sokoto Ya Gabatar Da Kasafin Fiye Da Naira Biliyan 700 Labarai
Ana Cigaba Da Tattaunawa Tsakanin Trump Da Zelensky Domin Tsagaita Wuta A Ukraine Labarai
Tinubu Ya Aika Manyan Hafsoshin Tsaro Borno Afrika
China Ta Kori Wakilan Majalisar Dokoki Uku A Kasar Labarai
Tsananta Hukunci Ga Masu Fyade Kan Takaita Cin Zarafin Yara Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Wani Dan Ta’adda Ya Hallaka ‘Yan Makaranta A Kasar Uganda
  • Sakataren Tsaron Amurka Ya Kori Shugaban Sojin Kasar
  • Kwararru Sun Nuna Damuwa Game Da Yakin Iran
  • Za’a Kada Kuri’a A Kwamitin Tsaro Na MDD Kan Yaki
  • Kasashen Da Dama Na Neman Hanyar Cigaba Da Dakon Makamashi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Angano Gawar Wani Dan Myanmar A Arewacin New York Afrika
  • An Kusa Kawo Karshen Matsalolin Tsaro A Jihar Filato Afrika
  • Wani Harin ‘Yan Bindiga Ya Kashe Mutane 35 A Jihar Borno Labarai
  • Kasar Rasha Ta Zargi Ukraine Da Kai Hari Gidan Shugaban Rasha Amurka
  • Kasashen Da Suke Kawance Da Amurka Sun Juyawa Trump Baya Afrika
  • Rundunan  ‘Yan Sandan Jihar Bauchi, Ta Miƙa Miyagun Ƙwayoyi Da Ta Kama Wa NDLEA. Labarai
  • Rasha Ta Nuna Kudurin Cimma Zaman Lafiya Da Ukraine Amurka
  • Shugaba Tinubu Ya Umurci Janyewa Manyan Mutane ‘Yan Sanda Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.