Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Gwamna Abba Kabir Ya Hana Yunkurin Kafa Sabuwar Hisba A Kano
Published: December 13, 2025 at 3:08 PM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: December 13, 2025

Gwamnatin Kano ta umarci jami’an tsaro su dakatar da masu yunkurin kafa hukumar Hisbah mai zaman kanta.

Gwamnatin Jihar Kano ta fitar da umarnin zantaswa da ya haramta wata kungiya da ke aiki da sunan “Independent Hisbah Fisabilillahi” Wannan umarni da Gwamna Abba Kabir Yusuf ya sanya wa hannu, mai dauke da ranar 8 ga Disamba, 2025, ya bayyana cewa gwamnati ta gano cewa ana ci gaba da daukar ma’aikata, horaswa da tura matasa cikin kungiyar ba tare da wata doka ko izini ba, kana kuma cikin sabawa dokar Hukumar Hisbah ta Jihar Kano.

Yayin da yake mika sakon ga manema labarai, Kwamishinan Yada Labarai da Harkokin Cikin Gida, Ibrahim Abdullahi Waiya, ya bayyana cewa Hukumar Hisbah ce kadai hukuma ta doka da ke da ikon jagorantar dukkan ayyukan Hisbah a fadin jihar.

Gwamnati ta ce bullar wannan kungiya ta daban wani yunkuri ne na kafa wata hukuma ba bisa ka’ida ba, lamarin da zai iya haifar da tashin hankali da kuma take matsayin hukumar Hisbah ta jihar.

Gwamnan ya kuma bayyana dukkan ayyukan kungiyar a matsayin “haramtattu, ba bisa doka ba kuma babu inganci,” yana gargadin cewa duk wani kaya da ya yi kamanceceniya da alamomi ko ikon Hukumar Hisbah zai fuskanci hukunci.

Gwamna Yusuf ya umarci Rundunar ‘Yansanda ta Najeriya, Hukumar DSS, NSCDC da sauran hukumomin tsaro da su binciki wadanda ke goyon bayan kungiyar, su dakatar da duk wani ci gaba da ake yi na daukar ma’aikata ko horaswa, sannan su dauki matakan da suka dace don hana tabarbarewar tsaro a jihar Kano.

Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya

Post navigation

Previous Post: Gidauniya: An Fara Tiyatar ‘Hernia’ Da ‘Hydrocele’ Kyauta A Jihar Katsina
Next Post: Anyi Jefe-Jefe Yayin Rangadin Messi, A Indiya

Karin Labarai Masu Alaka

Shugaba Tinubu Ya Gana Da Wasu Gwamnoni Shida Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Amurka Zata Hana Kwankwaso Shiga Kasar Amurka
Babangida: Hakika Abiola Ya Lashe Zaben Watan Yuni 1993 Labarai
Ministan Tsaron Najeriya Badaru Yayi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Sojoji Sun Yi Juyin Mulki A Guinea Bissau Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
An Yanke Mishi Hukuncin Kisa Saboda Neman Kudin Aure Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Wani Dan Ta’adda Ya Hallaka ‘Yan Makaranta A Kasar Uganda
  • Sakataren Tsaron Amurka Ya Kori Shugaban Sojin Kasar
  • Kwararru Sun Nuna Damuwa Game Da Yakin Iran
  • Za’a Kada Kuri’a A Kwamitin Tsaro Na MDD Kan Yaki
  • Kasashen Da Dama Na Neman Hanyar Cigaba Da Dakon Makamashi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Ko Arsenal Zata Iya Lashe Gasar Firimiya lig Na Bana Wasanni
  • Alhassan Yayi Nasarar Kifar Da Wurkilili A Gasar Damben Gargajiya Wasanni
  • Masar Tayi Yarjejeniyar Makamashi Da Kasashen Norway Da China Labarai
  • Fadar Shugaban Ƙasan Najeriya Ta Musanta Wani Labarin ƙarya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Shirin Dare 2030 UTC Yau Asabar 11.15.2025 Rediyo
  • Wasan Hamayya (Istanbul Derby) Fenerbahçe Da Galatasaray 1-1 Labarai
  • Wani Alkali A Amurka Ya Kalubalanci Gwamnatin Kasar Afrika
  • Kasar Aljeriya Ta Soke Yarjejeniyar Jirgin Sama Tsakaninta Da Daular Larabawa Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.