Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa Afrika
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa Afrika
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed Afrika

Kotu A Kasar Faransa Ta Daure Lumbala Shekaru 30 Bisa Laifin Cin Zarafi
Published: December 17, 2025 at 8:40 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Wata kotu a kasar Faransa ta yanke hukuncin daurin shekaru 30 a gidan kurkuku a kan tsohon madugun ‘yan tawayen Kwango ta Kinshasa, Roger Lumbala, wanda ta samu da laifuffukan cin zarafin bil Adama a lokacin yakin Kwango na biyu.

‘Yan rajin ganin an hukumta masu aikata irin wadannan laifuffuka a gadin duniya sun yaba da wannan hukunci a zaman babban ci gaba na hukumta masu hannu a wannan yakin da ya kashe miliyoyin mutane.

A lokacin da yake bayyana hukuncin, alkalin wannan kotu dake birnin Paris, Marc Sommerer, yace Lumbala ya aikata ko ya bada umurnin aikatawa, ko ya tallafa wajen aikata munanan laifuffuka da kashe-kashe da fyade, da gana azaba, da bautarwa da sata da wawusa ko lalata dukiyoyi.

Wadannan laifuffukan da aka tuhumi Lumbala da aikatawa suna da alaka da wani farmakin da wata kungiyarsa mai samun goyon bayan kasar uganda a lokacin, ta kai a shekarun 2002 da kuma 2003 a arewa maso gabashin Kwango.

Sun kai hare-haren ne a kan ‘yan kabilun Nande da Bambuti wadanda suka zarga da laifin goyon bayan wata kungiyar daban ta sojojin sa kai a yankin.

An gudanar da yakin Kwango na biyu daga shekarar 1998 zuwa 2003. Kasashe har guda 9 suka tsoma baki da hannu a wannan yaki, kuma an kashe mutane fiye da miliyan 5, cikinsu har da wadanda suka mutu a sanadin yunwa da kuma cututtuka.

Labarai

Post navigation

Previous Post: Wani Bayahude Ya Harbe Bafalatsine Dan Shekaru 16
Next Post: Gwamnatin Jihar Yobe: Ana Cin Zarafin Fursunoni A Gidan Gyaran Halin Potiskum

Karin Labarai Masu Alaka

Majalisar Wakilai Tayi Allah Wadai Da Hare-Haren ‘Yan Bindiga A Gombe Labarai
Kasar Faransa Ta Karyata Cire Afirka Ta Kudu Daga G7 Afrika
Ministan Sufurin Najeriya Ya Ajiye Mukaminsa Domin Takarar Gwamna Afrika
Hukumar ‘Yan Sanda Tayi Yarjejeniya Da ‘Yan Takara A Gombe Afrika
Jirage Marasa Matuka Sun Kaiwa Jiragen Ruwan Mai Hari A Gulf Afrika
Fiye Da Mutane 10 Sun Mutu A Hatsarin Hanyar Kano Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • NDLEA Ta Fara Binciken Kwakwaf Akan Wasu ‘Yan Mata Dake Kai Kwaya Gidan Yari Labarai
  • Ghana Tayi Watsi Da Yarjejeniya Akan Hakar Ma’adanai Afrika
  • Manchester United Ta Sallami Ruben Amorim Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Afirka Ta Kudu Ta Bayyana Yadda Aka Yaudari ‘Yan Kasar Ake Tilasta Musu Ayyukan Bauta Afrika
  • Barayin Waya Sun Yanke Yatsun Hannu Guda Biyu Da Gefen Kunne A Bauchi Labarai
  • Hamas Ta Mika Ma Isra’ila Gawar Daya Daga Cikin Mutane Biyu Sauran Duniya
  • Sallah Sai Ranar Juma’a A Najeriya: Fadar Sarkin Musulmi Afrika
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.