Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Rundunar ‘Yan Sandan Gombe Ta Kuɓutar da Yaro Daga Hannun Masu Garkuwa Afrika
  • Tinubu Ya Buɗe Katafaren Kamfanin Sarrafa Lithium Domin Bunƙasa Tattalin Arziki Afrika
  • Sojoji Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 1,597, Sun Ceto Mutane 1,516 – DHQ Afrika
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa Afrika

Shugaba Tinubu ya mika sunayen Sabbin Shugabannin NMDPRA da NUPRC Bayan Murabus Din Farouk Ahmad Da Gbenga Komolafe
Published: December 17, 2025 at 7:13 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Shugaba Tinubu ya mika sunayen Sabbin Shugabannin NMDPRA da NUPRC bayan murabus din Farouk Ahmad da Gbenga Komolafe

Shugaban Bola Ahmed Tinubu, ya aike wa Majalisar Dattawa sunayen mutane biyu domin tantancewa da amincewa a matsayin sababbin shugabannin hukumomin kula da harkokin mai da iskar gas na ƙasa.

Nadin ya biyo bayan murabus ɗin Injiniya Farouk Ahmed daga Hukumar Kula da Bangaren Mai da Gas na ƙasa (NMDPRA), da kuma Gbenga Komolafe daga Hukumar Kula da Hakar Mai ta Ƙasa (NUPRC).

An naɗa tsoffin Shugabannin ne a shekarar 2021 a zamanin tsohon Shugaba Muhammadu Buhari, bayan kafa hukumomin ƙarƙashin Dokar Masana’antar Man Fetur (PIA).

A wasiƙar da ya aike wa Majalisar Dattawa, Shugaba Tinubu ya nemi a gaggauta tantancewa da amincewa da Oritsemeyiwa Amanorisewo Eyesan a matsayin Babbar Darakta-Janar (CEO) ta NUPRC, da kuma Injiniya Saidu Aliyu Mohammed a matsayin Babban Darakta-Janar (CEO) na NMDPRA.

Eyesan ta kammala karatun Tattalin Arziki a Jami’ar Benin, kuma ta shafe kusan shekaru 33 tana aiki a Kamfanin Man Fetur na Ƙasa (NNPC) da rassa sannan ta yi ritaya a matsayin Mataimakiyar Shugabar Sashen Upstream (2023–2024), sannan ta rike mukamin Babbar Manaja ta Tsare-tsare da Dabaru daga 2019 zuwa 2023.

A nasa bangaren, Injiniya Saidu Aliyu Mohammed, haifaffen jihar Gombe a 1957, ya kammala digiri a fannin Injiniyan Sinadarai a Jami’ar Ahmadu Bello a 1981 kuma kwanan nan an sanar da shi a matsayin Darakta mai zaman kansa a kamfanin Seplat Energy.

Ya taba rike mukaman Darakta-Janar na Matatar Mai ta Kaduna da Kamfanin Iskar Gas na Najeriya, tare da shugabancin kwamitocin gudanarwa na West African Gas Pipeline Company.

Haka kuma, ya taba zama Darakta-Janar kuma Mataimakin Shugaban Ayyuka (COO) na Sashen Gas da Wutar Lantarki, inda ya taka rawa a manyan tsare-tsaren gas na ƙasa, ciki har da Gas Masterplan, Gas Network Code, da kuma bayar da gudummawa wajen tsara dokar PIA.

Injiniya Saidu Mohammed ya kasance cikin masu jagorantar manyan ayyuka kamar fadada bututun iskar gas na Escravos–Lagos, aikin bututun Ajaokuta–Kaduna–Kano (AKK), da ayyukan Nigeria LNG.

Najeriya

Post navigation

Previous Post: Ministan Kudin Najeriya: Bamu Samu Kudaden Da Muke Tsammani A Wannan Shekarar Ba
Next Post: SERVICOM, ATBUTH Ta Cafke Wani Da Ake Zargin Dan Damfara Ne

Karin Labarai Masu Alaka

Gwamnatin Tinubu Zata Samar Da Wutan Solar A Jami’ar ADUST Wudil Afrika
PDP Ta Tsayar da Goodluck Jonathan Takarar Shugaban Kasa Afrika
Jihar Ekiti Ta Aiwatar Da Dokar Haraji Najeriya
Za’a Gurfanar Da Sojojin Da Ake Zargi Da Yunkurin Juyin Mulki Najeriya
’Yar Kasuwa Ta Tsallake Rijiya Da Baya Bayan Hari Da Saurayinta Ya Kai Mata Afrika
An Saka Dokar Hana Fita A Jos Ta Arewa Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Rundunar ‘Yan Sandan Gombe Ta Kuɓutar da Yaro Daga Hannun Masu Garkuwa
  • Tinubu Ya Buɗe Katafaren Kamfanin Sarrafa Lithium Domin Bunƙasa Tattalin Arziki
  • Sojoji Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 1,597, Sun Ceto Mutane 1,516 – DHQ
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Kasar Amurka Ta Sayi Kamfanin Sada Zumunci Na Tik-Tok Amurka
  • Shugaba Bola Tinubu Ya Tafi Turai Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • An Sace Masu Ibada A Wata Majami’ar Ecwa A Jihar Kogi Tsaro
  • Muhimmin Sako Ga Alhazai Dake Kasar Saudiya Afrika
  • Sabunta Manhajar Ilimi A Duk Matakai Nasara Ce! Najeriya
  • Yanbindiga sun Kashe mutun guda tare da yin garkuwa da mutane kimanin 100 a Jihar Nejan Najeriya. Najeriya
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Turkiyya Ta Zargi Alakar Isra’ila Da Somaliya Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.