Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Gwamnan Gombe Ya Taya Sarkin Musulmi Murnar Cika Shekaru 70, Ya Yi Masa Addu’ar Ƙarin Lafiya Da Tsawon Rai Afrika
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika

Shugaba Tinubu ya mika sunayen Sabbin Shugabannin NMDPRA da NUPRC Bayan Murabus Din Farouk Ahmad Da Gbenga Komolafe
Published: December 17, 2025 at 7:13 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Shugaba Tinubu ya mika sunayen Sabbin Shugabannin NMDPRA da NUPRC bayan murabus din Farouk Ahmad da Gbenga Komolafe

Shugaban Bola Ahmed Tinubu, ya aike wa Majalisar Dattawa sunayen mutane biyu domin tantancewa da amincewa a matsayin sababbin shugabannin hukumomin kula da harkokin mai da iskar gas na ƙasa.

Nadin ya biyo bayan murabus ɗin Injiniya Farouk Ahmed daga Hukumar Kula da Bangaren Mai da Gas na ƙasa (NMDPRA), da kuma Gbenga Komolafe daga Hukumar Kula da Hakar Mai ta Ƙasa (NUPRC).

An naɗa tsoffin Shugabannin ne a shekarar 2021 a zamanin tsohon Shugaba Muhammadu Buhari, bayan kafa hukumomin ƙarƙashin Dokar Masana’antar Man Fetur (PIA).

A wasiƙar da ya aike wa Majalisar Dattawa, Shugaba Tinubu ya nemi a gaggauta tantancewa da amincewa da Oritsemeyiwa Amanorisewo Eyesan a matsayin Babbar Darakta-Janar (CEO) ta NUPRC, da kuma Injiniya Saidu Aliyu Mohammed a matsayin Babban Darakta-Janar (CEO) na NMDPRA.

Eyesan ta kammala karatun Tattalin Arziki a Jami’ar Benin, kuma ta shafe kusan shekaru 33 tana aiki a Kamfanin Man Fetur na Ƙasa (NNPC) da rassa sannan ta yi ritaya a matsayin Mataimakiyar Shugabar Sashen Upstream (2023–2024), sannan ta rike mukamin Babbar Manaja ta Tsare-tsare da Dabaru daga 2019 zuwa 2023.

A nasa bangaren, Injiniya Saidu Aliyu Mohammed, haifaffen jihar Gombe a 1957, ya kammala digiri a fannin Injiniyan Sinadarai a Jami’ar Ahmadu Bello a 1981 kuma kwanan nan an sanar da shi a matsayin Darakta mai zaman kansa a kamfanin Seplat Energy.

Ya taba rike mukaman Darakta-Janar na Matatar Mai ta Kaduna da Kamfanin Iskar Gas na Najeriya, tare da shugabancin kwamitocin gudanarwa na West African Gas Pipeline Company.

Haka kuma, ya taba zama Darakta-Janar kuma Mataimakin Shugaban Ayyuka (COO) na Sashen Gas da Wutar Lantarki, inda ya taka rawa a manyan tsare-tsaren gas na ƙasa, ciki har da Gas Masterplan, Gas Network Code, da kuma bayar da gudummawa wajen tsara dokar PIA.

Injiniya Saidu Mohammed ya kasance cikin masu jagorantar manyan ayyuka kamar fadada bututun iskar gas na Escravos–Lagos, aikin bututun Ajaokuta–Kaduna–Kano (AKK), da ayyukan Nigeria LNG.

Najeriya

Post navigation

Previous Post: Ministan Kudin Najeriya: Bamu Samu Kudaden Da Muke Tsammani A Wannan Shekarar Ba
Next Post: SERVICOM, ATBUTH Ta Cafke Wani Da Ake Zargin Dan Damfara Ne

Karin Labarai Masu Alaka

Tinubu Ya Buɗe Katafaren Kamfanin Sarrafa Lithium Domin Bunƙasa Tattalin Arziki Afrika
Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika
Sojoji Sun Ceto Mutane 23, Sun Hallaka ’Yan Ta’adda 19 A Cikin Sa’o’i 24 Afrika
Shugaba Bola Tinubu Ya Tafi Turai Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Ana Cigaba Da Bincike Game Da Mutuwar Matar Da Likita Ya Manta Almakashi A Cikinta A Kano Najeriya
An Kusa Kawo Karshen Matsalolin Tsaro A Jihar Filato Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Alejandro Balde Na Dab Da Komawa Manchester United Daga Barcelona
  • Kocin Newcastle Matthias Ya Ce Lewis Hall Ba Zai Koma Manchester United Ba
  • Dan Wasan Baya Na Chelsea, Disasi, Zai Yi Gwajin Lafiyarsa A Crystal Palace
  • Gwamnan Gombe Ya Taya Sarkin Musulmi Murnar Cika Shekaru 70, Ya Yi Masa Addu’ar Ƙarin Lafiya Da Tsawon Rai
  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Allah Ya Yiwa Shahararren Dan Jarida Saleh Shehu Ashaka Rasuwa Labarai
  • Harin Isra’ila A Gaza Da Jirgi Maras Matuki Ya Kashe Mutane Afrika
  • Amurka Na Shirin Kauracewa Taron Kungiyar Kasashen G20 Afrika
  • Shirin Safe 0500 UTC Yau Asabar 11.22.2025 Rediyo
  • An Yanke Hukuncin Kisa Ga Hasina Tsohuwar Firaiy-Ministan Bangladash Labarai
  • Kungiyar Maharba Da ‘Yan Sintiri Sun Samu Kyautar Motoci Labarai
  • TIC Dutse Ta Nemi Ƙarin Tallafin Gwamnatin Jigawa Don Faɗaɗa Ayyukanta Afrika
  • Al’ummar Jihar Nasarawa Suna Cecekuce Bisa Tsaida Aliyu Wadada Takarar Gwamna Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.