Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

Kudi Sunfi Rayuwar Mutum Muhimmanci A Asibitocin Najeriya
Published: December 19, 2025 at 2:24 AM | By: Yusuf Aliyu Harande | Updated: December 19, 2025

Abuja- Jami’ar kula da dakin yara ta babban asibitin Maraba a jihar Nasarawa NAS Rita Danjuma ta ce yaran talakawa wato jarirai na shiga wani hali in rashin lafiya ya same su don rashin kudin saya mu su magani.

Likitar ta ce wani lokacin duk kokarin da su ke yi lamarin ya kan gagara don rashin samun abubuwan da a ke nema don taimakawa yaran kasancewar iyayen yaran ba su da wadatar kudi.

Rita Danjuma da ke magana lokacin da wata kumgiyar jinkai KHADIJA ENTERTAINMENT ta kai kayan tallafi dakin yaran; ta ce ya na da kyau duk masu dan sukuni su rika ziyartar asibitoci don ganin abun da za su tabuka.

Wannan ma kokarin na yiwuwa ne daidai gwargwado a asibitocin gwamnati da talakawa ke iya zuwa jinya “sai dai mu na iyakacin kokarinmu sai mu ba su shawara a kan a samu a nema sai ka ga wani lokaci ma da shi ke ba kudi sai ka ga wani har mutuwa ya na kai wa saboda ba magani ba wani abu da za mu yi don magani da an dan samu an saya ba zai iya kai su ba, wadansunsu har ya na kai ga mutuwa. Kar a manta a zo a na dan lekawa a na taimakawa wadanda ba su da hannu da shuni da za su iya tamakawa kan su.”

Mun ci karo da wani magidanci mai suna Alhassan Abdullahi da ya kawo matarsa don a yi ma ta aikin tiyatar gaggawa amma rashin kudi ya sa shi rikicewa a harabar asibitin don an ba shi adadin kudi Naira 55,000 da kuma kudin magani Naira 20,000 inda ya samu ya sayo magani na Naira 10,000 ya saura da Naira 10 kacal a aljihunsa.

Hajiya Adama Mai Agogo da ta kawo tallafin ta ce ba sai mai hannu da shuni kadai zai iya taimakawa ba “an ce ka gayyaci mai zuciya buki ba mai kudi ba.”

Kan hanyar fita daga asibitin mai gadi Sulaiman Abdullahi ya sanar da mu cewa akwai wani bawan Allah da wasu abokan sa su ka kawo amma yayin da likita ke rubuta maganin da za a sayo sai su ka faki ido su ka gudu inda shi kuma ya riga mu gidan gaskiya bayan ‘yan makonni.

Hakika mutane na zuwa asibiti kullum tamkar yanda su ke shiga kasuwa don sai da lafiya a ke yin motsi da ya fi labewa.

https://gtahausa.com/wp-content/uploads/2025/12/HUMAN-ANGLE-SUPPORT-TO-PEDITRIC-UNIT-MARABA-MEDICAL-CENTER.mp3
Kiwon Lafiya

Post navigation

Previous Post: Fintiri: Zamu Maida Jihar Adamawa Sabuwar Duniya
Next Post: Tinubu: Ku Guji Yi Wadaka Da Kudin Kananan Hukumomi

Karin Labarai Masu Alaka

Pads To Prosperity: NEDC Ta Horar Da Mata 280 Kan Kera Pads A Gombe Afrika
NANPAN Ta Wayar Da Al’umma Kan Amfanin Shayar Da Jarirai Nono Kaɗai Afrika
Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa Afrika
Hukumar NDLEA Ta Lalata Gonakin Wiwi A Ekiti Afrika
Rashin Hanya da Asibiti Ya Jawo Asarar Rayuka A Jihar Gombe – Sarkin Gargajiya Afrika
Gwamnatin Tinubu Ta Warware Basussukan Fansho Na Shekaru 18 Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Sakamakon Rikicin Gabas Ta Tsakiya Farashin Mai Ya Karu Labarai
  • Jaura Ta Bayyana A Wasu Jihohin Amurka Labarai
  • Gwamnan Jihar Bauchi Ya Jagoranci Tsohon Shugaban Kasar Najeriya Rangadi A Bauchi Afrika
  • Jagoran Adawar Uganda Bobi Wine Ya Fice Daga Kasar Afrika
  • Tsohon Shugaban Brazil Bolsanaro Zai Tafi Gidan Yari Labarai
  • Isra’ila Takai Hare Hare Birnin Tehran Afrika
  • Janar Christopher Zai Maye Gurbin Ministan Tsaron Najeriya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Harin Ukraine Yayi Mummunan Barna A Rasha Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.