Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19 Afrika
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027 Afrika
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki Afrika
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko Afrika

Rasha Ta Nuna Kudurin Cimma Zaman Lafiya Da Ukraine
Published: December 22, 2025 at 5:42 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Wakilin Amurka na musamman, Steve Witkoff, yace ana samun ci gaba a tattaunawar da Amurka take yi da Ukraine da kasashen Turai a gefe guda, da kuma wadda take yi da kasar Rasha a daya gefen, duk da nufin kawo karshen yakin Rasha da Ukraine.

Amurka da Ukraine da kuma kasashen Turai sun shafe kwanaki ukun da suka shige suna tattaunawa a jihar florida a kan yadda zasu fito da matsaya guda game da rikicin na Ukraine.

A bayan da suka gana da Kirill Dmitriev, wakilin shugaba Vladimir Putin na Rasha na musamman ran asabar a Miami, Witkoff da mashawarcin Trump, Jared Kushner, sun gana ranar lahadi da wakilan Ukraine da Turai, sannan daga bisani suka gana su kadai da wakilan Ukraine karkashin jagorancin Rustem Umerov.

Witkoff ya fada cikin wata sanarwar da ya rubuta a shafin sada zumunta cewa tattaunawar ta lahadi ta yi ma’ana da amfani, ta kuma mayar da hankali a kan yadda Amurka da Turai da kuma Ukraine zasu tinkari lamarin da murya guda.

A wata sanarwar dabam da ya buga a shafin sada zumunta na X, Witkoff yace Rasha ta nuna cewa har yanzu kudurinta shine na cimma zaman lafiya a Ukraine.

Tunda fari a lahadin, jami’in tsara manufofin hulda da kasashen waje na fadar Kremlin, Yuri Ushakov, yace irin shawarwarin da Ukraine da kasashen Turai suka bayar game da shirin da ake tattaunawa a kai, ba su karfafa guiwar yiwuwar cimma zaman lafiya ba, amma yace an shirya Dmitriev zai koma birnin Moscow yau litinin domin yi masa bayani game da tattaunawar da aka yi.

UShakov yace bayan nan zasu zauna su tsara yadda su ma zasu tunkari lamarin

Amurka

Post navigation

Previous Post: Hari Akan Wata Mashaya Ya Rutsa Da Mutane 9 A Afirka Ta Kudu
Next Post: Yau Litinin Ake Cigaba Da Shari’ar Najib Zarak

Karin Labarai Masu Alaka

Shirin Kwace Iyakar Greenland Da Shugaba Trump Yakeyi Yabawa Kasashen Turai Mamaki Amurka
Farashin Mai Yana Cigaba Da Karuwa Afrika
Shugaban Kasar Iran Yace Kasar Bata Da Kiyayya Tsakaninta Da Amurkawa Afrika
Amurka Ta Jefa Makamin Tomahawk A Makarantar Yara Mata Afrika
Kasashen Faransa Da Italiya Sun Nuna Rashin Amincewa Da Matakan Sojoji Amurka
Shugaba Trump Yayi Barazanar Tarwatsa Cibiyar Makamashin Iran Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • GOSEMA Ta Horar Da Mambobin LEMCs A Jihar Gombe Afrika
  • Jam’iyar APC A Jihar Gombe Ta Tsayar Da Jamilu Isiyaku Gwamna Takarar Gwamna Afrika
  • Nada Jakadu Da Tinubu Yayi Sako Ne Ga ‘Yan-Arewa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ana Jimamin Mutuwar Giwa Mai Shekaru Kusan 60 A Kasar Kenya Sauran Duniya
  • A Kowacce Rana Kasar China Tana Sayan Danyen Mai Ganga Dubu 600 Daga Kasar Venezuela Amurka
  • Zamfara: Sai Mun Hada Kai Don Kawo Karshen Ta’addanci Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Tarayya Zata Fara Gwajin Shan Kwaya Kafun Daukar Aiki Kiwon Lafiya
  • Asusun IMF Ya Bukaci Afirka Ta Kudu Ta Rage Bashin Da Suke Karba Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.