Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Najeriya Ta Dauki Hayan Amurkawa Don Kyautata Alaka Da Trump Game Da Kisan Kiristoci Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Tarayya Ta Cimma Yarjejeniya Da Kungiyar Malaman Jami’oi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Amurka Ta Baiwa Najeriya Wasu Muhimman Kayan Yaki Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Trump Yayi Kira Ga ‘Yan Ƙasar Iran Su Ci Gaba Da Zanga Zanga Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Syria: Mutane Sun Yi Zanga Zanga Domin Nuna Rashin Amincewa Da Korar Kurdawa A Birnin Aleppo Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Jami’an Tsaro: Babu Abun Tashin Hankali Kan Shawagin Jiragen Amurka
Published: December 23, 2025 at 2:29 AM | By: Yusuf Aliyu Harande | Updated: December 23, 2025

Wasu jami’an tsaron Najeriya sun bada tabbaci ga ‘yan kasar cewa babu wani abun tashin hankali ko fargaba gameda jiragen leken asiri na Amurka da suke shawagi a sararrin samaniyar kasar. Suka ce matakin ya faranta musu rai saboda Amurka tana taimakawa Najeriya ne ta fuskar tsaro.

Jami’an tsaron sun tabbatarwa Amurka Ke Magana cewa matakin na hadin gwiwa ne tsaknin jami’an tsaron Amurka da mayakan sama na Najeriya. Suka ce akwai sojojin sama na Najeriya a cikin jiragen da suke aikin leken asirin a sararin samaniyar kasar.

Jiragen suna tashi ne daga Ghana. Wannan matakin ya biyo bayan shawarwari da jami’an gwamnatin Najeriya suka yi da gwamnatin Amurka, bayan da shugaban Amurka Donald Trump, yayi barazanar kai hari kan Najeriya domin kare kiristocin kasar wadanda ake zargin ana yi musu kisn kare dangi. Gwamnatin Trump ta amince zata taimaki Najeriya ne bayan da aka gabatar mata da irin kalubale da kasar take fuskanta ta fuskar tsaro.

Gameda zargin gwamnatin Najeriya tana biyan kudin fansa kamin a saki mutane da ake garkuwa da su, musamman dalibai daga makarantu da ‘yan bindiga suke sace su, jami’an tsaron sun rantse da Allah cewa babu sisin kwabo daga aljihun Najeriya da yake fita domin biyan kudin fansa.

Daga nan suka yi kira ga ‘yan Najeriya su daina yi wa matakan gwamnati bahaguwar fahimta, maimakon haka a kullum su bukaci bayani, kamin su yanke shawara kan batu da  ya shafi gwamnati da al’uma.

Kamfanin dillancin labarai na Reuters ya buga labarin zirga-zirgar jiragen leken asirin  sararin samaniyar Najeriya.

Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Najeriya

Post navigation

Previous Post: An Samu Nasarar Karbo Karin Yara 130 Daga Hannun ‘Yan-Ta’adda
Next Post: Afirka Ta Kudu Ta Bayyana Yadda Aka Yaudari ‘Yan Kasar Ake Tilasta Musu Ayyukan Bauta

Karin Labarai Masu Alaka

Tinubu: Ku Guji Yi Wadaka Da Kudin Kananan Hukumomi Najeriya
Janar Christopher Zai Maye Gurbin Ministan Tsaron Najeriya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Syria: Mutane Sun Yi Zanga Zanga Domin Nuna Rashin Amincewa Da Korar Kurdawa A Birnin Aleppo Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Jami’an Tsaro Na Amfani Da Damar Su Wajen Cin Zarafin Jama’a Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Anyi Girgizar Kasa Mai Karfi A Kasar Mexico Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Wata Mace Ta Mutu A Hannun ‘Yan-Fashin Daji, Wata Ta Haihu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Najeriya Ta Dauki Hayan Amurkawa Don Kyautata Alaka Da Trump Game Da Kisan Kiristoci
  • Gwamnatin Tarayya Ta Cimma Yarjejeniya Da Kungiyar Malaman Jami’oi
  • Kabiru Vice: Najeriya Zata Iya Nasara A Kan Moroko AFCON 2025.
  • Motar Yashi Ta Kashe Mutane Shida A Wani Coci Dake Legas
  • An Kaddamar Da Rijistar Zamani Ta Zamowa Mamba A Jam’iyar APC

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Shirin: Lafiya Jari Ce 11.21.25 Kiwon Lafiya
  • An tura tsohon ministan Ilimin Nijar gidan yari saboda zargin aikata fyade ga wata daliba. Afrika
  • Allah Ya Yi Wa Sheikh Dahiru Bauchi Rasuwa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • An Kai Hari Kan Masu Hakar Ma’adanai A Kasar Mali Tsaro
  • NUJ: Akwai Bukatar Samar Da Inshorar Lafiya Ga ‘Yan Jarida A Najeriya Rediyo
  • Rasha Da Ukraine Sun Cigaba Da Yakar Juna Afrika
  • Wasan Hamayya (Istanbul Derby) Fenerbahçe Da Galatasaray 1-1 Labarai
  • Kasar Botswana Na Samun Kudaden Shiga Da Lu’ulu’u Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.