Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika

Guinea An Zabi Madugun Sojojin Da Suka yi Juyin Mulki Mamady A Shugaban Ƙasar,
Published: January 1, 2026 at 10:31 AM | By: Bala Hassan

 Ƙasar Guinea kuma an zabi Mamady Doumbuya, madugun sojojin da suka yi juyin mulki a zaman shugaban kasa, kamar yadda kwarya-kwaryar sakamakon zabe da aka bayyana jiya talata, mataki da ya kammala shirin maido da kasar kan turbar demokuradiyya, ga kasar dake Afirka ta yamma da Allah Ya yiwa albarkar karfe. 

Tsohon kwamandan dakaru na musamman, wanda ake kiyasin dan shekaru 40 ne da haifuwa, Dumbouya ya yiwa shugaba Alpha Conde wanda yake shugabancin kasar tun 2010 juyin mulki shekara ta 2021. Juyin mulkin na kwango yana daga cikin jerin sauye sauye gwamnati da bakin bindiga har tara a kasashe da suke yammaci da kuma wadanda suke yankin tsakiyar Afirka daga shekara ta 2020.

Kwarya-kwaryar sakamakon zaben da aka bayar a  talata, ya nuna shugaba Doumbuya ya sami kashi 86.7 cikin dari na kuriu da aka kada, a zaben da aka yi ranar 28 ga watan Disemban 2025, rinjaye mai karfi da zata hana shi zuwa zagaye na biyu a zaben,

Tuni dai ake sa ran shugaba Doumbuya ya sami nasara a zaben, domin tsohon shugaban kasa Alpha Conde, da dadadden shugaban ‘yan hamayya Cellou Dalein Diallo suke gudun hijira, wadda ya baiwa shugaba Doumbuya damar fuskantar tsirarun ‘yan hamayya da suka kasa hada kai su takwas.

Kotun kolin kasar tana da kwanaki takwas ta tabbatar da sakamakon zaben, idan har akwai wadanda suke jayayya kan wannnan sakamako.

Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Post navigation

Previous Post: ‘Yansandan Uganda Sun Tsare ‘Yar Fafutukar Kare Hakkin Bil’adama Sarah Bireete
Next Post: Tinubu Yace Zayyi Hadaka Da Kasashen Duniya Domin Kawo Karshen Rashin Tsaro.

Karin Labarai Masu Alaka

Sanata Goje: Sakamakon Zaben Daga Abuja Zai Fito Afrika
An Bukaci Matasa Su Taka Gagarumar Rawa Wajen Gina Zaman Lafiya A Arewa Maso Gabas Afrika
Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
‘Yan Agajin Izalar Jos Sunyi Hatsari Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Najeriya Ta Dauki Hayan Amurkawa Don Kyautata Alaka Da Trump Game Da Kisan Kiristoci Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
An Gano Gawar Dan Yawon Bude Ido A Kasar Chadi Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Najeriya Ta Kai Wasan Kusa Da Na Karshe A Wasan Dambe Na Matasan Afirka Wasanni
  • Gwamna Ahmad Aliyu Na Jihar Sokoto Ya Gabatar Da Kasafin Fiye Da Naira Biliyan 700 Labarai
  • SERVICOM, ATBUTH Ta Cafke Wani Da Ake Zargin Dan Damfara Ne Labarai
  • An Garkame Dan Majalisa Watannin Takwas A Kasar Tunisiya Afrika
  • NUJ: Akwai Bukatar Inganta Albashin ‘Yan Jarida A Najeriya Najeriya
  • Kasar Uganda Ta Tsare ‘Yan Jam’iyyun Adawa Dubu Biyu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • NUT Ta Shiga Yajin Aikin Sai Baba Ta Gani Afrika
  • Bayan Ya Ziyarci Kwankwaso Gawuna Zai Karbi Katin ADC Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.