Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi Afrika
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19 Afrika
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027 Afrika
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki Afrika
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko Afrika

Tinubu: Abba Magajin Aminu Kano Ne A Fagen Siyasa
Published: January 4, 2026 at 7:08 PM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: January 4, 2026

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya bayyana Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, a matsayin magajin Malam Aminu Kano wajen kishin al’umma da jajircewa kan walwalar jihar Kano.

Tinubu ya bayyana hakan ne cikin wani saƙon taya murna da ya aike wa gwamnan bisa cika shekaru 63 da haihuwa.

Wannan na kunshe ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban ƙasa, Bayo Onanuga, ya fitar a ranar Lahadi.

A cewar Shugaba Tinubu, sauƙin kai, tawali’u da kuma jajircewar Gwamna Abba Kabir Yusuf sun bayyana karara a yadda yake tafiyar da al’amuran mulki a jihar Kano.

Shugaban ƙasar ya ƙara da cewa yana da cikakken tabbaci cewa Gwamna Yusuf yana bin sahun hangen nesa da tafarkin Malam Aminu Kano wajen jagorancin jihar, wadda ke da muhimmiyar rawa a siyasar Arewacin Najeriya.

Tinubu ya ce jajircewar gwamnan wajen kare haƙƙin talakawan birni da na karkara na daga cikin manyan dalilan da ke tabbatar da hakan.

A cewarsa, shirye-shiryen sabunta birane da gwamnatin Kano ta ɓullo da su, musamman gina gadoji da tituna masu tsawon kilomita biyar biyar a kowace ƙaramar hukuma, sun nuna ƙwazon shugabancin gwamnan.

Haka kuma, Shugaba Tinubu ya yaba da ayyana dokar ta baci da Gwamna Yusuf ya yi a ɓangaren ilimi, inda ya ce hakan ya haifar da gagarumar ci gaba, musamman yadda ɗaliban jihar Kano suka samu sakamako mai kyau a jarabawar NECO.

A ƙarshe, Shugaba Tinubu ya yi wa Gwamna Abba Kabir Yusuf fatan tsawon rai da ƙarin shekaru na shugabanci masu albarka, tare da fatan ganin ƙarin ci gaba da bunƙasuwar jihar Kano.

Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu, Siyasa

Post navigation

Previous Post: ‘Yan Agajin Izalar Jos Sunyi Hatsari
Next Post: Shugaba Trump Yace Amurka Ce Zata Rika Gudanar Da Harkokin Kasar Venezuela

Karin Labarai Masu Alaka

Farashin Mai Ya Fadi Fiye Da Dala Daya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Gwamna Kefas Na Jihar Taraba Ya Karbi Shaidar Jam’iyar APC Siyasa
Gwamna Abba Kabir Ya Zabi Garo A Matsayin Mataimaki Afrika
“Hotuna” An Sako Daliban Makarantar St. Mary’s Su 100 Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
Maulidin 2026: IMC Ta Yi Kira Da Ƙarfafa Zaman Lafiya Da Haɗin Kai A Najeriya Afrika
PDP Ta Koka Kan Rushe-rushe, Korar Gombawa Motors da Zaɓen Kananan Hukumomi A Gombe Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ’Yan Sandan Gombe Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane Da Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Gwamnan Gombe Ya Rantsar Da Sabbin Manyan Sakatarori 19
  • CBCN Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu A Zaɓen 2027
  • Gwamna Bala Mohammed Ya Miƙa Ta’aziyyar Rasuwar Abdullahi Sule Madaki
  • Al’ummar Wajari Sun Amfana Da Gyaran Cibiyar Kiwon Lafiya Matakin Farko

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • ‘Yan Wasan Kwallon Kafar Najeriya A Shirye Suke Wasanni
  • Chukwueze, Ya Ci Gaba Da Riƙe Rigarsa Mai Lamba 21 A AC Milan Wasanni
  • Fanny Amun Ya Yi Murabus A Matsayin Shugaban Kwamitin Binciken NFF Wasanni
  • FRSC Gombe: Hatsarin Mota Ya Yayi Ajalin Mutane 38 Ya Jikkata Fiye Da 218 A Wata Ɗaya Najeriya
  • Guinea Bissau Ta Tsaida Gwaje-Gwajen Allurar Rigakafin Shawara A Kasar Labarai
  • Iran Da Amurka Zasu Kulla Yarjejeniyar Nukiliya Amurka
  • Shirin Safe 0500 UTC Yau Talata 11.18.2025 Rediyo
  • Shugaban Kare Hakkin Dan Adam Na Majalisar Dinkin Duniya Yace RSF Sun Aikata Zalunci Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.