Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • PDP Ta Tsayar da Goodluck Jonathan Takarar Shugaban Kasa Afrika
  • Hawan Gidan Gwamnati A Jihar Gombe Afrika
  • Hawan Babbar Sallah A Masarautar Kaltungo Dake Jihar Gombe Afrika
  • Sarkin Gombe Ya Yabi Nasarorin Inuwa Yahaya A Fannonin Tsaro Da Raya Kasa Afrika
  • Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi Afrika

Koriya Ta Arewa Ta Gudanar Da Gwajin Makami Mai Linzami
Published: January 5, 2026 at 5:35 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Kamfanin dillancin labaran Koriya ta Arewa, ya ba da rahoton cewa ranar lahadi, kasar ta gudanar da gwajin harba makamai masu linzami masu tsananin gudu, a wani matakin auna irin karfin sojojinta da makamansu na kare kai.

Shugaba Kim Jong Un, wanda ya sanya idanu wajen harba makaman, yace mataki ne mai matukar muhimmanci ga kasar ta ci gaba da kasancewa tana da karfin makaman nukiliya, ko ta fadada su, domin zamowa hannunka mai sanda ga duk mai neman kai mata farmaki.

Kamfanin dillancin labaran na KCNA yace makaman sun fada kan inda aka auna su kimanin kilomita dubu daya a tekun dake gabas da Koriya ta Arewa.

A ranar lahadi, rundunar sojojin Koriya ta Kudu, ta ce Arewa ta harba makamai masu linzami a tekun dake gabas da kasar a daidai lokacin da shugaban Koriya ta Kudu, Lee Jae Myung ya fara ziyarar aiki a kasar China.

Harba wadannan makamai masu linzami masu tsananin gudu da Koriya ta Arewa ta yi, ya biyo bayan fitowar da ta yi tana yin Allah wadarai da harin da Amurka ta kai a kan Venezuela a zaman wanda ya keta haddin diyaucin kasar.

Tsaro

Post navigation

Previous Post: Shugaba Trump Yace Amurka Ce Zata Rika Gudanar Da Harkokin Kasar Venezuela
Next Post: Kasar Botswana Na Samun Kudaden Shiga Da Lu’ulu’u

Karin Labarai Masu Alaka

Kurdawa Sun Gargadi ‘Yan Uwansu Game Da Alaka Da Amurka Wajen Yakar Iran Afrika
Babban Sakataren MDD Yayi Allah Wadai Da Matakin Soja A Gabas Ta Tsakiya Afrika
Yanayin Sanyi Yayi Kamari a Yankin Gaza Tsaro
‘Yan Tawayen Houthi Sunkai Hari Isra’ila Afrika
Ana Zargin Wani Dan Kasar Libya Da Fataucin Mutane Tsaro
EFCC Ta Tsare Tsohon Minista Abubakar Malami Tsaro

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • PDP Ta Tsayar da Goodluck Jonathan Takarar Shugaban Kasa
  • Hawan Gidan Gwamnati A Jihar Gombe
  • Hawan Babbar Sallah A Masarautar Kaltungo Dake Jihar Gombe
  • Sarkin Gombe Ya Yabi Nasarorin Inuwa Yahaya A Fannonin Tsaro Da Raya Kasa
  • Tinubu Ya Jaddada Aniyar Rage Tsadar Rayuwa Da Samar da Ayyukan Yi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Ana Cigaba Da Samun Hare Hare Da Jiragen Marasa Matuki A Sudan Labarai
  • An Zargi Kasar Eritrea Da Cin Zarafin Sojojin Habasha Afrika
  • Na Yi Murabus Ne Don Amurka Ta Keta Haddin Iraniyawa Amurka
  • An Zargi Babban Mai Gabatar Da Kara A Kotun Duniya Ta ICC Afrika
  • Matatar Man Dangote Zata Bada Kwangilar Sayar Da Gas Da Man Jirage Afrika
  • ‘Yan Kasashen Afirka Da Dama Suna Fafatawa Da Rasha A Yaki Da Ukraine Afrika
  • ECOWAS Zata Kafa Rundunar Yaki Da Rashin Tsaro Afrika
  • ‘Yan Ta’adda Sun Tarwatsa Wani Kauye A Jihar Sakkwato Tsaro
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.