Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnan Gombe Yace An Sace Yara 48 A Jihar Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

An tura tsohon ministan Ilimin Nijar gidan yari saboda zargin aikata fyade ga wata daliba.
Published: January 8, 2026 at 1:38 PM | By: Mustapha Nasiru Batsari | Updated: January 8, 2026

Hukumomi a Jamhuriyar Nijar sun cafke tsofon ministan ilimi mai zurfi PhD Mamadou Djibo sakamakon zargin yi wa wata daliba fyade. Tuni a ka wuce da shi gidan yari a ci gaba da binciken wannan al’amari da ta farfado da mahawwara game da cin zarafi mata a makarantu.
Wakilin GTA Hausa Amurka ke Magana Souley Moumouni Barma ya aiko mana Karin bayani daga birnin Yamai.
Ainahi tsofon minista Mamodou Djibo ya gurfana a ofishin ‘yan sandan farin kaya inda aka saurare shi bayan da wata daliba ta shigar da kara a bisa zarginsa da yi ma ta fyade. Daga bisani maganar ta kara gaba zuwa kotu inda alkali mai tuhuma ya damka shi a hannun alkali mai bincike wanne ya tura shi gidan yarin Kollo a ci gaba da bincike. abinda ‘yan kasa ke ganin alama ce ta yunkurin zartas da abubuwan da dokokin kasa suka yi tanadi dangane da batun cin zarafin mata. Alhaji Abdou Maman Lokoko na daga cikin shugabanin kungiyoyin bunkasa ilimi a Nijar.

Majiyoyi na cewa dalibar da ta bankado wannan badakala na daga cikin daliban makarantar da ke karatu a makarantar tsofon minista PhD Mamadou Djibo lamarin da ke farfado da mahawwara game da yanayin da dalibai mata ke karatu cikinsa. Wata ‘yar fafutika Housseina Maizoumbou na ganin lokaci ya yi da za a kawo karshen matsalar.

A nan gaba ne a ke saran gurfanar da tsohon ministan na ilimi a gaban alkali domin tantance zahirin abubuwan da suka faru.
Dan rajin kare hakkin dan adam Abdourahamane Oumarou na cewa…

Kawo yanzu ba wani takamemen bayani daga bangaren mashara’anta haka kuma wani makusancin ministan da ke zargi ko laiyansa ba su ce kala ba game da wannan dambarwa.

An tura tsohon ministan Ilimin Nijar gidan yari saboda zargin aikata fyade.

https://gtahausa.com/wp-content/uploads/2026/01/TSOHON-MINISTA-NIJAR.mp3
Afrika

Post navigation

Previous Post: Amurka Ta Kama Tsohon Ministan Kudin Kasar Ghana
Next Post: Sarkin Kagarko Ya Rasu Yana Da Shekaru 110

Karin Labarai Masu Alaka

Wakilan Majalisar Dokokin Phillipines Suna Yunkurin Tsige Shugaban Kasar Afrika
Harin Jirgi Marar Matuki Ya Kashe Kakakin ‘Yan Tawayen M23 Afrika
Gwamnatin Sojan Burkina Faso Ta Soke Jam’iyyun Siyasar Kasar Afrika
Harin Makami Mai Linzami Da Rasha Ta Kai Yayi Barna Sosai A Ukraine Afrika
Afirka Ta Kudu Ta Samu Rigakafin Cutar Boro Afrika
Sojoji Sunkai Farmaki Gidan Dan Adawa A Kasar Uganda Bobi Wine Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ‘Yan Uwa Musulmi A Jihar Gombe Sunyi Allah Wadai Da Kisan Ayatollah Khomeini
  • An Samu Kaburbura Biyu Dauke Da Gawarwaki 173 A Kasar Kwango
  • Yan Bindiga Suna Cigaba Da Kashe Mutane A Garin Gwana Dake Jihar Bauchi
  • Karancin Iskar Gas Kalubale Ne Ga Wutar Lantarki
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Shugaban Kasar Najeriya Ya Gabatar Da Kudi Fiye Da Naira Triliyan 58 A Matsayin Kasafin 2026 Najeriya
  • Guinea Bissau Ta Tsaida Gwaje-Gwajen Allurar Rigakafin Shawara A Kasar Labarai
  • Shirin Safe 0500 UTC Yau Asabar 11.15.2025 Rediyo
  • ‘Yan Sanda Sun Kama Mutane Takwas Da Ake Zargi Da Siyar Da Tikitin AFCON Ba Bisa Ka’ida Ba Wasanni
  • Rikici Ya Barke A Kano Bayan Kashe Wani Matashi Da Ake Zargi Da Kashe Ladani Najeriya
  • Gwamnatin Bauchi: Ta Kaddamar Da Kwamitin Ma’adanai Labarai
  • Shirin Dare 2030 UTC Yau Litinin 11.17.2025 Rediyo
  • Rundunar ‘Yan Sanda Sun Ceto Wani Daga Hannun Masu Garkuwa Najeriya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.