Hukumomi a Jamhuriyar Nijar sun cafke tsofon ministan ilimi mai zurfi PhD Mamadou Djibo sakamakon zargin yi wa wata daliba fyade. Tuni a ka wuce da shi gidan yari a ci gaba da binciken wannan al’amari da ta farfado da mahawwara game da cin zarafi mata a makarantu.
Wakilin GTA Hausa Amurka ke Magana Souley Moumouni Barma ya aiko mana Karin bayani daga birnin Yamai.
Ainahi tsofon minista Mamodou Djibo ya gurfana a ofishin ‘yan sandan farin kaya inda aka saurare shi bayan da wata daliba ta shigar da kara a bisa zarginsa da yi ma ta fyade. Daga bisani maganar ta kara gaba zuwa kotu inda alkali mai tuhuma ya damka shi a hannun alkali mai bincike wanne ya tura shi gidan yarin Kollo a ci gaba da bincike. abinda ‘yan kasa ke ganin alama ce ta yunkurin zartas da abubuwan da dokokin kasa suka yi tanadi dangane da batun cin zarafin mata. Alhaji Abdou Maman Lokoko na daga cikin shugabanin kungiyoyin bunkasa ilimi a Nijar.Majiyoyi na cewa dalibar da ta bankado wannan badakala na daga cikin daliban makarantar da ke karatu a makarantar tsofon minista PhD Mamadou Djibo lamarin da ke farfado da mahawwara game da yanayin da dalibai mata ke karatu cikinsa. Wata ‘yar fafutika Housseina Maizoumbou na ganin lokaci ya yi da za a kawo karshen matsalar.
A nan gaba ne a ke saran gurfanar da tsohon ministan na ilimi a gaban alkali domin tantance zahirin abubuwan da suka faru.
Dan rajin kare hakkin dan adam Abdourahamane Oumarou na cewa…Kawo yanzu ba wani takamemen bayani daga bangaren mashara’anta haka kuma wani makusancin ministan da ke zargi ko laiyansa ba su ce kala ba game da wannan dambarwa.


