Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama Afrika
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara Afrika
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe Afrika
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa Afrika

Shugaba Trump Ya Hana Kaiwa Cuba Man Fetur Daga Venezuela
Published: January 12, 2026 at 9:15 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Ranar lahadi shugaba Donald Trump na Amurka yace babu man fetur ko sisin kwabo na Venezuela da zai sake zuwa Cuba, yana mai cewa ya kamata shugabannin kwaminis na kasar su nemi kulla yarjejeniya da Amurka kafin lokaci ya kure.

Kasar Cuba tana samun mafi yawan man fetur dinta daga Venezuela, amma babu jirgin mai ko guda daya da ya tashi zuwa Cuba daga can tun bayan da sojojin Amurka suka damko shugaba Nicolas Maduro.

Shugaba Miguel Diaz-Canel na Cuba yayi watsi da barazanar da shugaba Trump yayi a kafofin sada zumunci, yana mai cewa ai Amurka ba ta da hurumin sanya Cuba ta kulla wata yarjejeniya.

Diaz-Canel ya fada a shafin X cewa Cuba, kasa ce ‘yantacciya, mai cin gashin kai, kuma babu wani mahalukin da zai fada mata ga abinda zata yi.

Yace Cuba ba ta kai hari, amma Amurka ta yi shekaru 66 tana kai mata farmaki, yana mai fadin cewa a shirye suke su ci gaba da kare kasarsu.

Amurka

Post navigation

Previous Post: Masar Tayi Yarjejeniyar Makamashi Da Kasashen Norway Da China
Next Post: Barcelona Ta Lashe Kofin Spanish Super Cup 

Karin Labarai Masu Alaka

Baital Malin Amurka Tace Sahannun Trump Zai Fito A Kudin Kasar Amurka
Shugaba Trump Yace Bazai Bari Iran Ta Mallaki Nukiliya Ba Amurka
Ukraine Tana Cigaba Da Tattaunawa Da Amurka Domin Kawo Karshen Yakin Kasar Amurka
Farashin Danyen Mai A Amurka Ya Tashi Afrika
Afirka Ta Kudu Tace Bazata Yanke Alaka Da Iran Ba Afrika
Gwamnatin Amurka Tana Ganawa Da Manyan Jami’an Leken Asiri Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Sojojin Najeriya Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda Da Dama
  • An Sace Wani Shugaban Karamar Hukuma A Jihar Zamfara
  • Aikin Tsaftar Muhalli Na Wata-Wata Ya Samu Gagarumar Nasara A Gombe
  • Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro
  • Gombe Ta Haɗa Kai Da UNICEF Don Kare Yara Daga Tamowa Tun Kafin Haihuwa

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Bankin Duniya Ya Rage Hasashen Bunkasar Tattalin Arzikin Afirka Da Yankin Sahara Afrika
  • Gwamnatin Tinubu Ta Karyata Kafa Kamfanin Gwal A Legas Labarai
  • Hawan Durba A Fadar Sarkin Zazzau Afrika
  • Tinubu, Akpabio da Ministoci 9 Zasu Tafi Ƙasar Birtaniya Afrika
  • Ranar Lahadi Anyi Zaben Shugaban Kasa A Congo Afrika
  • Masu Kare Hakkin ‘Yan Gudun Hijira A Amurka Sun Mika Koke Amurka
  • An Gudanar da Taron Kwana Biyu kan Tsarin Sa Ido da Tantance Ayyukan AGILE a Jihar Gombe  Afrika
  • Kayan Jinya Da Ayyukan Kiwon Lafiya Suna Barazanar Karewa A Sudan Kiwon Lafiya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.