Najeriya ta shiga rukuni na karfafa ci gaba da ta samu ta fuskar tattalin arziki, bayan sauye sauye na shekaru biyu da gwamnatin kasar ta kaddamar, wadanda suka taimaka wajen tsaida hauhawar farashin kayayyaki, ya kawo daidaito kan darajar kudi, wadanda suka karfafawa masu zuba jari guiwa, kamar yadda ministan kudi Wale Edun ya fada a ranar Alhamis.
Tunda ya kama mulki a shekara ta 2023, shugaba Tinubu ya bullo da shirye shirye masu karfi na sauya fasalin tattalin arzikin kasar da aka dade sosai ba’a ga irinsu ba, da suka hada da janye tallafin man fetur, ya rage darajar kudin kasar har sau biyu, da kuma sauya dokar haraji da zummar bunkasa kudaden shiga ga gwamnati.
Matakan sun kawo matsanancin tsadar rayuwa da aka jima ba’a ga irinsa ba, amma suka inganta alkaluman tattalin arziki, sai dai kuma manyan kungiyoyin kwadagon kasar sunce matakan sun jefa membobin su cikin wani mawuyacin halin rayuwa, inda hauhawar farashin kayayyaki ya durkusar da ma’aikata saboda, albashin su baya biyan bukata.
Ministan kudi Wale Edun, yace Najeriya ta doshi tudun mun tsira, bayan fadi tashin da tattalin arzikin kasar ya shiga sakamakon janye tallafin man fetur da gyaran fuska ga tafarkin canjin kudin kasar.


