An dakatar da tsohon tauraron kwallon kafa na Kamaru Samuel Eto’o na wasanni hudu tare da cin tararsa dala $20,000 (£14,960) bayan kwamitin ladabtarwa na Hukumar Kwallon Kafa ta Afirka (Caf) ya same shi da laifin rashin da’a.
Sanarwar Caf ta ce Eto’o, wanda yanzu shine shugaban hukumar kwallon kafa ta kasarsa Kamaru (Fecafoot), ya karya ka’idojinta na wasanni a lokacin wasan kusa da na karshe na gasar cin kofin kasashen Afirka ta 2025 tsakanin Kamaru da Morocco.
An ruwaito cewa tsohon dan wasan gaban Barcelona da Inter Milan ya nuna fushinsa kan wasu daga cikin shawarwarin da jami’an suka yanke yayin da Indomitable Lions ta sha kashi 2-0 a hannun masu masaukin baki Ƙasar Moroko.
Shugaban Caf Patrice Motsepe, wanda shi ma ya halarci filin wasa da ke Rabat, ya shaida faruwar abun inda ya nuna takaicin sa ga me da Eto’o.
A ranar Litinin hukumar gudanarwa ta nahiyar ta sanar da fara bincike kan “tashin hankali da kuma halayyar da ba a yarda da ita ba ta wasu ‘yan wasa da jami’ai” a wasannin ƙungiyoyi takwas na gasar ta AFCON.
A martanin da ta mayar, hukumar kwallon kafa ta Kamaru Fecafoot ta yi watsi da matakin na Caf, inda ta bayyana tsarin amatsayin abun shakku game da buƙatan shari’a mai adalci”.
Sannan Fecafoot ta nuna goyon bayanta ga shugabanta a cikin wata sanarwa a ranar Laraba, yayin da ta nuna cewa Eto’o zai daukaka kara kan hukuncin.
Tun bayan da ya hau kan mukaminsa a shekarar 2021, an lalata tasirin Eto’o a matsayin gwarzon wasan saboda wasu hayaniya da ke da alaka da badakala da matsaniya.
Inda ya fuskanci zarge-zargen rashin da’a da rashin kyakkyawan shugabanci, wasu masu ruwa da tsaki a kwallon kafa suma ke korafin manyan kura-kurai a cikin Fecafoot.
A yayin tantance ‘yan wasa da zasu wakilci Ƙasar Kamaru a gasar cin kofin kasashen Afirka da ke guda na a Moroko an zargi Eto’o da sanya baki wajan kawo sunayen wadda ya ke so yayin da ya ceri wadda ake ganin basa shiri irin su maitsaron ragar Manchester United Andrew Onana, da Vincent Abubakar.
Sai dai Eto’o ya sha musanta irin wadannan zarge-zargen, yana mai bayyana nasarorin da aka samu a matsayin shugaban Hukumar.


