kasar Turkiyya na gudanar da bincike game da kona tutar ta a yayin da wasu kungiyar kurdawa ke zanga-zanga a wajajen iyakar ta da kasar Sham, a daidai lokacin da sojojin Sham ke gwabza fada da dakarun kurdawa.
Dakarun sojin Sham sun kara zurfafawa cikin wuraren da kurdawa ke rike da madafun iko ranar Talata, bayan da suka kwace yankuna da ‘Yan tawayen kurdawan na SDF suka dade suna rike da ikon su. Wannan ya dabbaka shirin shugaba ahmed al-Sharaa na Sham wajen hada kan kasar kan tafarkin mulki daya.
Fadar gwamnatin Turkiyya a Ankara da ta kasance jigo wajen marawa shugaba al-Sharaa baya, ta dauki ‘yan tawayen kurdawan na SDF a matsayin ‘yan ta’adda, kuma ta sha cewa dole su hade da sauran ‘yan kasar Sham karkashin gwamnati daya.


