An ja hankalin tsohon Shugaban Kasar Najeriya Olushegun Obasanjo kan wasu kalaman kiyayya da yake yi wa Atiku Abubakar
Suvr. Lawal Jahun Chiroman Galadiman Bauchi tsohon Malamin Kwalejin kimiya da fasaha na gwamnatin tarayyar Najeriya dake Bauchi shine yayi wannan kira ga Obasanjo, a wata hira da yayi da GTA Hausa.
Lawal yace Obasanjo yanzu a Najeriya shi uba ne saboda haka kowa nasane bai da ce da wasu kalamai na nuna cewa Atiku Abubakar bai cancanci zama Shugaban ƙasa ba.
Mun san cewa Atiku yayi mataimaki wa Obasanjo na tsawon shekaru takwas duk da cewa an san sun kare dutse a hannun riga amman Atiku ya taimaki Obasanjo a lokacin da ya ke niman tazarce, shi ya shawo kan Gwamnoni musan na arewa yace suyi hakuri su sake zaban Obasanjo karo na biyu
An sani cewar duk shugaba yana da yadda za’a yaba masa bisa wasu ayyukan cigaba da ya kawo a kwai kuma yadda ya gaza saboda shi dan adam ne tara yake bai cika goma ba.
A lokacin Obasanjo cigaba da aka samu a shi ne bangaren tsaro da kuma yaki da yunwa, wannan kowa yasani amman a inda yagaza shine ya halarta wa gwamnonin jihohi su karbi kudin kananan Hukumomin wadda ya jawo kananan Hukumomin suka fita hayyacinsu a yanzu haka.
Matsalolin da aka samu tsakanin tsohon mataimakin shugaban ƙasa Atiku da Obasanjo ai shi Atiku yayi tattaki har zuwa gidan gonan Obasanjo domin su dai dai ta amman Obasanjo yaki ” Inji Suvr Lawal.
Amman abunda muka fahinta shine Obasanjo yana kin Atiku ne saboda yana tsoron kar ya tona masa wani asiri tunda sunyi aiki tare ya san wasu sirrinsa, ko kuma ya na tsoron kar ya rama abunda ya masa duk da bama son a yi mulki na ramukon gayya.
Saboda haka idan Obasanjo bazai goyi bayan Atiku ba to ya bari al’umar ƙasa su zabi wadda suke so domin su za’a mulka.
Lawal ya kara da cewa yanzu a Najeriya babu wani kamar tsohon mataimakin shugaban ƙasa Atiku Abubakar in dai batun siyasa ne haka kuma a jihar Bauchi Baba kamar Air vice Marshal Sadiq Baba Abubakar ritaya.


