Gwamnatin kasar Sham ta ce harin da kungiyar ‘yan tawayen kurdawa ta SDF ta kai wa dakarun ta da jiragen drone ya yi sanadiyar hallaka sojoji 7 ranar laraba duk da kungiyar SDF din sun musanta hakan.
Wannan abu na barazanar kawo koma baya ga yarjejeniyar tsagaita wuta da bangarorin biyu suka kulla, bayan da suka shafe kwanaki suna gwabza kazamin fada.
Sojin Sham sun ce, wannan harin da aka kai yayin da dakarun nasu ke neman killace wani sansanin sojoji da aka kame mai dauke da bama bamai, tunzura ce me hadari.
Kungiyar ta SDF ta ce bata kai hari ba, ta ce an samu fashewar bama bamai ne lokacin da sojojin Sham ke kokarin matsar su. Ta kuma zargi sojojin na Sham da karya alkawarin yarjejeniyar zaman lafiya hanyar kai hare-hare a wurare da dama.
Bayan shafe kwanaki tana ci gaba da samun nasara, gwamnatin Sham ta ce ran Talata, ta cimma fahimta tsakanin ta da dakarun SDF, don yarda da yarjejeniyar tsagaita wuta na kwana hudu, kuma su yarda su kasance karkashin mulkin gwamnatin, ko kuma a ci gaba da kai musu farmaki a birane biyu da suka rage musu da suke rike da madafun iko.


