Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Jarman Deba Ya Kada Senata Goje A Zaben Fidda Gwani Afrika
  • Jami’an ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayi Afrika
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai Afrika
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika

Gwamnatin Sham Tace Harin Kurdawa Ya Hallaka Sojojin Kasar
Published: January 21, 2026 at 9:36 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

Gwamnatin kasar Sham ta ce harin da kungiyar ‘yan tawayen kurdawa ta SDF ta kai wa dakarun ta da jiragen drone ya yi sanadiyar hallaka sojoji 7 ranar laraba duk da kungiyar SDF din sun musanta hakan.

Wannan abu na barazanar kawo koma baya ga yarjejeniyar tsagaita wuta da bangarorin biyu suka kulla, bayan da suka shafe kwanaki suna gwabza kazamin fada.

Sojin Sham sun ce, wannan harin da aka kai yayin da dakarun nasu ke neman killace wani sansanin sojoji da aka kame mai dauke da bama bamai, tunzura ce me hadari.

Kungiyar ta SDF ta ce bata kai hari ba, ta ce an samu fashewar bama bamai ne lokacin da sojojin Sham ke kokarin matsar su. Ta kuma zargi sojojin na Sham da karya alkawarin yarjejeniyar zaman lafiya hanyar kai hare-hare a wurare da dama.

Bayan shafe kwanaki tana ci gaba da samun nasara, gwamnatin Sham ta ce ran Talata, ta cimma fahimta tsakanin ta da dakarun SDF, don yarda da yarjejeniyar tsagaita wuta na kwana hudu, kuma su yarda su kasance karkashin mulkin gwamnatin, ko kuma a ci gaba da kai musu farmaki a birane biyu da suka rage musu da suke rike da madafun iko.

Afrika, Labarai

Post navigation

Previous Post: Harin Jirgi Maras Matuki Ya Hallaka Mutane A Sudan
Next Post: ‘Yan Kasar Venuzuela Zasu Fara Komawa Gida

Karin Labarai Masu Alaka

Gwamnatin Somaliya Da MDD Sun Bayyana Cewa Kimanin Mutane Miliyan Shida Da Rabi Suna Fuskantar Barazanar Yunwa Labarai
Darajar Kudin Afirka Ta Kudu Ya Tashi Afrika
Donald Trump Yace Basu Cimma Matsaya Da Benjamin Natanyahu Ba Afrika
Jirgin Ruwan ‘Yan Gudun Hijira Ya Nitse Kogi A Tunisiya Labarai
Zulum Ya Rushe Majalisar Zartarwa Ta Jihar Borno Afrika
Harin Da Israela Ta Kai Gaza Yayi Ajalin Mutane 27 Da Yara Uku Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jarman Deba Ya Kada Senata Goje A Zaben Fidda Gwani
  • Jami’an ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayi
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Yaki Tsakanin Amurka, Isra’ila Da Iran Ya Shiga Kwana Na Biyar Afrika
  • Zamu Hana Wasu ‘Yan-Najeriya Visa Shiga Amurka Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Gombe Ta Raba Naira Miliyan 14 Ga Iyalen ‘Yan Jaridan Da Suka Rasu Najeriya
  • China Da Jamhuriyar Dimokraɗiyya Kwango Sun Kulla Yarjejeniya Afrika
  • Magajin Garin Istanbul Dake Kurkuku Ya Bukaci A Gudanar Da Zabe Labarai
  • Shugaban Kasar Amurka Yakara Hana Wasu Kasashe Shiga Amurka Ciki Harda Nijar Amurka
  • CAF Ta Hukunta Samuel Eto’o AFCON 2025 Labarai
  • Kasar Chadi Ta Rufe Iyakar Ta Da Kasar Sudan Afrika
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.