Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maikaba Ya Yi Murabus A Matsayinsa Kocin Wikki Tourist FC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • NEDC : Zata Samar Da Cikekken Kulawa Wa ‘Yan Jaridar Da Sukayi Hatsari A Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Trump Zata Kafa Kasuwar Ma’adanai Amurka
  • An Yanke Mishi Hukuncin Kisa Saboda Neman Kudin Aure Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Babban Malamin Musulunci Sheikh Usman Kusfa Zaria Ya Rasu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Za’a Gurfanar Da Sojojin Da Ake Zargi Da Yunkurin Juyin Mulki
Published: January 26, 2026 at 8:38 PM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: January 28, 2026

Binciken da rundunar sojin Nigeria ta yi ya gano akwai yiwuwar cewa wasu dakarun ta 16 da aka kama shekarar da ta gabata saboda aikata laifi, suna shirin kifar da gwamnati ne ta hanyar juyin mulki, kuma zasu fuskanci shari’a, a cewar wani jawabi da ya fito daga babban ofishin tsaro na kasa a ranar litinin.

Jawabin ya ce binciken da aka yi ya binciko sahihan abubuwa a kan da yawa daga cikin sojojin, ciki har da zargin shirin hambarar da gwamnati, amma bai bada bayanin yadda shirin nasu yake ba, da ko sojoji nawa daga cikin 16 ne ke da hannu ciki ba.

Mai magana da yawun hukumar tsaro major janar Samaila Uba, ya ce an tsare Jami’an sojojin a watan Octobar bara, wadanda kuma ake tuhumar su da laifin yunkurin Juyin mulki yanzu za’a tsayar da su gaban alkalin kotun soja. Ya kara da cewa, idan an kama su da laifi, zasu fuskanci hukuncin kisa.

A watan Octoba na shekarar da ta wuce ne, Shugaba Bola Tinubu ya sauya sojoji masu rike da manyan mukamai da wasu, a yunkurin sa na karfafa matakan tsaro, yayin da kasar ke fuskantar barazana daga kungiyoyin ‘yan ta’adda da dama.

Najeriya

Post navigation

Previous Post: Abba Kabir Yusuf Ya Koma Jam’iyar APC
Next Post: Kungiyar ‘Yan Ta’adda Masu Alaka Da ISIS Sun Kashe Mutane A Congo

Karin Labarai Masu Alaka

NUJ: Akwai Bukatar Inganta Albashin ‘Yan Jarida A Najeriya Najeriya
CBN: An Samu Ƙaruwar Masu Cin Bashin Banki Basa Biya Najeriya
Amurka Ta Nuna Damuwa Kan Matsalar ‘Yan Gudun Hijira A Najeriya Najeriya
‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane A Hare Hare Daban Daban A Najeriya Najeriya
Ga Fili Ga Doki Najeriya
Mizanin Tattalin Arzikin Najeriya Na 2024 Ya Karu Da Kashi 3.84% Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ‘Yan Bindiga Sun Karya Alkawarin Dakatar Da Kai Hare Hare A Najeriya
  • Amurka Zata Bawa Sojojin Najeriya Horo
  • Indonesia Zata Kafafa Rundunar Kiyaye Zaman Lafiya A Gaza
  • Shugabannin Kasar Australia Sun Bukaci ‘Yan Kasar Suyi Zanga Zanga Cikin Lumana
  • Shugaban Afrika Ta Kudu Yanuna Goyon Bayan Kawo Karshen Yaki Tsakanin Rasha Da Ukraine

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • ‘Yan Tawayen Kungiyar M23 Sun Tsagaita Sakamakon Rokon Da Amurka Tayi Amurka
  • Wata Tankar Mai Ta Kife A Apapa Legas Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • An Sace Masu Ibada A Wata Majami’ar Ecwa A Jihar Kogi Tsaro
  • Masana: ‘Yancin Kasashen Afrika A Rubuce Yake Ba A Zahirance Ba Najeriya
  • Kasar Gambiya Ta Gayawa Kotun MDD Shirin Myanmar Akan Musulmai Afrika
  • Janar Christopher Zai Maye Gurbin Ministan Tsaron Najeriya Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Fubara Yana Yiwa Dimokraɗiyya Zagon Kasa Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Amurka Da Najeriya Sunyi Hadakar Inganta Asibiticin Kiristoci Amurka
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.