‘Yan sanda 3 sun rasa rayukan su, yayin da wasu 2 suka jikkata lokacin da ‘yan ta’adda dauke da makamai suka kai hari kan ‘yan sanda masu sintiri a jihar Katsinan Najeriya ranar Talata, a cewar ‘yan sanda ranar laraba.
Wannan na daga cikin karuwar hare-hare da ‘yan ta’adda ke kaiwa, da ya hada da garkuwa da mutane da ‘yan bindiga ke yi idan sun far wa makarantun da wuraren ibada, a arewa maso yammacin kasar.
Mai magana da yawun ‘yan sandan jihar Katsina, Abubakar Sadiq Aliyu ya ce an far ma ‘yan sandan ne a wajen hanyar Guga da Bakori lokacin da suke sintiri. Ya ce ‘yan sandan sun nuna jarumta sosai wajen mai da wuta, inda suka fattattaki ‘yan ta’addan, amma sun rasa jami’ai uku a musayar wuta. ‘Yan sanda biyu da suka samu raunuka na karbar magani a wani asibiti da ke kusa da inda abun ya faru.
A wani labarin kuma, a dai Najeria, a yau ‘yan sanda a jihar Lagos sun harbawa masu zanga-zanga kan rushe sansanin gidajen talakawa dake gab da teku da gwamnatin jihar ta yi tear gas, inda daya daga cikin masu zanga-zangar ya samu rauni. Rushe gine-ginen ya jawo da dubbannan mutane rasa matsugunin su.
Jami’ai a jihar Lagos, tare da taimakon ‘yan sanda da mashunan tonon kasa, sun fara rushe gidajen talakawa a unguwar Makoko, inda suka ce mazauna wurin sun gina gidajen nasu ne ba bisa ka’ida ba, wadanda yawanci gidajen katako ne aka gina su a saman ruwa, kusa da injunan lantarki masu hatsari.


