Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maikaba Ya Yi Murabus A Matsayinsa Kocin Wikki Tourist FC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • NEDC : Zata Samar Da Cikekken Kulawa Wa ‘Yan Jaridar Da Sukayi Hatsari A Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Trump Zata Kafa Kasuwar Ma’adanai Amurka
  • An Yanke Mishi Hukuncin Kisa Saboda Neman Kudin Aure Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Babban Malamin Musulunci Sheikh Usman Kusfa Zaria Ya Rasu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

‘Yan Ta’adda Sun Kashe ‘Yan Sanda A Jihar Katsina
Published: January 28, 2026 at 7:48 PM | By: Aliyu Bala Gerengi

‘Yan sanda 3 sun rasa rayukan su, yayin da wasu 2 suka jikkata lokacin da ‘yan ta’adda dauke da makamai suka kai hari kan ‘yan sanda masu sintiri a jihar Katsinan Najeriya ranar Talata, a cewar ‘yan sanda ranar laraba.

Wannan na daga cikin karuwar hare-hare da ‘yan ta’adda ke kaiwa, da ya hada da garkuwa da mutane da ‘yan bindiga ke yi idan sun far wa makarantun da wuraren ibada, a arewa maso yammacin kasar.

Mai magana da yawun ‘yan sandan jihar Katsina, Abubakar Sadiq Aliyu ya ce an far ma ‘yan sandan ne a wajen hanyar Guga da Bakori lokacin da suke sintiri. Ya ce ‘yan sandan sun nuna jarumta sosai wajen mai da wuta, inda suka fattattaki ‘yan ta’addan, amma sun rasa jami’ai uku a musayar wuta. ‘Yan sanda biyu da suka samu raunuka na karbar magani a wani asibiti da ke kusa da inda abun ya faru.

A wani labarin kuma, a dai Najeria, a yau ‘yan sanda a jihar Lagos sun harbawa masu zanga-zanga kan rushe sansanin gidajen talakawa dake gab da teku da gwamnatin jihar ta yi tear gas, inda daya daga cikin masu zanga-zangar ya samu rauni. Rushe gine-ginen ya jawo da dubbannan mutane rasa matsugunin su.

Jami’ai a jihar Lagos, tare da taimakon ‘yan sanda da mashunan tonon kasa, sun fara rushe gidajen talakawa a unguwar Makoko, inda suka ce mazauna wurin sun gina gidajen nasu ne ba bisa ka’ida ba, wadanda yawanci gidajen katako ne aka gina su a saman ruwa, kusa da injunan lantarki masu hatsari.

Najeriya, Tsaro

Post navigation

Previous Post: Kotu A Kasar Uganda Ta Bada Belin ‘Yar Gwagwarmaya
Next Post: Maganganun Jami’an Shige Da Fice Dana Shugaban Kasa Trump Suna Cin Karo Da Juna

Karin Labarai Masu Alaka

Majalisar Tattalin Arzikin Najeriya Ta Bawa Gwamnan Kebbi Mukamin Kyautata Harkar Kiwo Najeriya
Muna Kokarin Kawo Karshen Cin Zarafin Jinsi A Gombe – Uwargidan Gwamna Labarai
Shugaba Tinubu Ya Gabatar da Kasafin Kuɗin 2026 Najeriya
Kamfanin NNPC Yana Tattaunawa Da Wani Kamfanin Kasar China Labarai
Majalisar Wakilai Tayi Allah Wadai Da Hare-Haren ‘Yan Bindiga A Gombe Labarai
Sojojin Najeriya Sun Kwato Mutane Daga Hannun Masu Garkuwa Najeriya

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ‘Yan Bindiga Sun Karya Alkawarin Dakatar Da Kai Hare Hare A Najeriya
  • Amurka Zata Bawa Sojojin Najeriya Horo
  • Indonesia Zata Kafafa Rundunar Kiyaye Zaman Lafiya A Gaza
  • Shugabannin Kasar Australia Sun Bukaci ‘Yan Kasar Suyi Zanga Zanga Cikin Lumana
  • Shugaban Afrika Ta Kudu Yanuna Goyon Bayan Kawo Karshen Yaki Tsakanin Rasha Da Ukraine

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Masu Kare Hakkin ‘Yan Gudun Hijira A Amurka Sun Mika Koke Amurka
  • Kotun Kasar Rasha Ta Daure Dan Kasar Belarus Shekarar 22 A Kurkuku Labarai
  • Amurka Ta Kwace Jirgin Mai Mallakar Rasha Amurka
  • Kamfanin Hakar Ma’adanai Na Kasar Kanada Ya Cigaban Da Aikinsa Labarai
  • Kasashen Duniya Sunyi Tir Da Hambarar Da Gwamnatin Venezuela Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Kungiyar Kiristoci Ta Wanke Gwamnan Bauchi Daga Zargin Ta’addanci Labarai
  • Kasar Tanzaniya Zata Gina Babban Tashar Iskar Gas Labarai
  • Gwamnatin Tarayya Ta Ce Babu Musguna Wa ’Yan Jarida A Mulkin Tinubu Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.