Fiye da mutane 200 suka rasa rayukansu sakamakon rushewar wani kogo na hakar ma’adanai a Jamhuriyar Demokradiyar Congo. Lumumba Kambere, wanda shi ne gwamnan da kungiyar ‘yan tawaye suka nada a yankin da abin ya faru, ya shaidawa kamfanin dillancin labarai na Reuters cewa hatsarin ya afku ne a Wurin hakar ma’adanai na Rubaya, inda ake hako ma’adanin coltan.

Wurin hakar ma’adanan na Rubaya na samar da kashi 15 cikin 100 na ma’adanin coltan a fadin duniya, wanda ake sarrafashi zuwa wani ma’adanin da ake kira tantalum a turance, wanda ya ke da jure Zafi, kuma ake amfani da shi wajen kera wayoyin hannu, computoci, sassan jiragen sama da injunan gas. Gurin da mutanen gari ke aikin haka ana biyan su kudi kadan, ya kasance karkashin ikon kungiyoyin tawaye na AFC da M23 tun shekarar 2024.
Rugujewar kogon ya afku ne ranar Laraba, kuma har zuwa Jumu’a ba’a san ainihin adadin rayukan da suka salwanta ba.


