Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

‘Yan Jarida Sunyi Mummunan Hatsari A Bauchi
Published: February 6, 2026 at 12:57 PM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: February 6, 2026

Daga Ahmad Muhammad,Bauchi

‘Yan jarida kimanin su 14 da suka fito daga kafafen yada labarai dabam -dabam suka gamu da mummunar hatsarin mota a yayin da suke cikin tawagar hukumar raya yankin Arewa Maso Gabas (NEDC)

Shugaban kungiyar Yan Jarida Na kasa reshen jihar Bauchi da ke Arewa maso gabashin Najeriya Kwamred Umar Said ya tabbatar da aukuwar lamarin.

Umar Said wanda yake jagorantan aikin  yace tare suke tafiya , direban motar Yana gudu Sai taqwace ta Tashi sama ta shiga daji kafin daga bisani tayi ta dungure dasu tana zubar da mutanen da ke ciki har Allah ya tsaida su.

Ya nuna godiya wa Allah saboda ba a rasa rai ko daya ba a ciki amma an Samu munanan raunuka da asarar kayayyakin Aiki”

Ya godewa Ministan Uba Maigari Ahmadu , da Mataimakin Gwamnan Jihar Bauchi Muhammadu Awwal Jatau, da Shugaba da Manajin Darektan Hukumar NEDC sauran Ma’aikatan Hukumar da ‘Yanjaridu saboda yadda suka nuna damuwarsu kan abinda ya faru da Kuma yadda suka tsaya Kan lamarin.

Lokacin da abin ya faru Yan jaridun suna tafiya ne a ƙarƙashin jagorancin ƙaramin ministan raya yankuna, Alhaji Uba Maigari Ahmadu a yayin da suke yawon buɗewa da miƙa ayyukan da hukumar NEDC ta gudanar a jihar Bauchi zuwa hannun gwamnatin jihar.

Hatsarin ya faru ne a kan titin Yashi zuwa Yelwan Duguri da ke cikin ƙaramar hukumar Alkaleri a jihar Bauchi da ke tarayyar Najeriya a yau ranar Jumma’a, bayan ministan ya qaddamar da katafaren makaranta a garin Yalwan Duguri.

‘yan jaridun sun samu munanan raunuka raunuka daban-daban yayin da ake ƙoƙarin samar musu da agajin gaggawa a asibitin Yelwan Duguri daga bisani kuma za a wuce da su babban asibiti a Bauchi domin neman musu kulawar likitoci.

‘Yan jaridun da abin ya Shafa waɗanda suka fito daga gidajen talabijin na Channels, AIT, NTA, BATV,Arise da wasu irin su wakilan manyan jaridun na Guardian, the nation, kamfanin dillancin labarai Na Nijeriya (News agency of Nigeria) (NAN) da sauransu da dama.

Hatsarin ya faru ne jimkaɗan bayan da tawagar suka buɗe aikin makarantar GSS a Yelwan Duguri inda suke kan hanyarsu ta zuwa domin buɗe wasu ayyukan.

Daga cikin waɗanda suke cikin tawagar har da minista, shugabannin NEDC, chairman da MD, mataimakin gwamnan jihar Bauchi da sauransu.

Kazalika, Wakilinmu wanda ke cikin tawagar ya shaida mana cewa motar da ta gamu da hatsarin ɗaya ce daga cikin motocin da ‘yan jaridan ke amfani da su a yayin aikin ɗauko labarin. Ya kuma tabbatar mana da cewa kayayyakin aikin jarida dama kamar su Kamarori sun lalace. Amma Babu asarar rai.

Labarai, Najeriya

Post navigation

Previous Post: Jakadan Amurka A Poland Ya Yanke Hulda Da Kakakin Majalisar Kasar
Next Post: Tawagar Shirya Gasar Kwallon Sarakuna A Gombe Ta Ziyarci Masarautun Jihar

Karin Labarai Masu Alaka

Makarantun Allo Zasu Yi Gogayya Da Na Boko Labarai
Jaura Ta Bayyana A Wasu Jihohin Amurka Labarai
Shugaban Amurka Zai Sake Gine Gaza Amurka
Anyi Rashin ‘Yan Jarida 6 A Jihar Gombe Sakamakon Hatsarin Mota Labarai
Hukumar ICPC Ta Gayyaci Dangote Labarai
Tinubu Ya Sake Fasalin Rundunar Sojin Ƙasa Domin Inganta Tsaro Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Majalisa Ta Sanya Baki Akan Rikici Tsakanin Dangote Da Hukumar Albarkatun Mai Najeriya
  • Shugaban Amurka Donald Trump Yace Bai Taba Shiga Jirgin Jeffrey Epstein Ba Labarai
  • Kasashen Da Dama Na Neman Hanyar Cigaba Da Dakon Makamashi Afrika
  • Rundunar Wanzar Da Zaman Lafiya Zata Tabbatar Da Tsagaita Wuta A Kwango Afrika
  • Gaza Ga Albarusai Ga Yunwa Tsaro
  • Gwamnatin Najeriya Zata Samar Da Sabbin Dakunan Karatun Dalibai Afrika
  • Wani Abu Ya Fashe A Ofishin Jakadancin Amurka Dake Kasar Norway Afrika
  • An Sako Ɗaliban Makaranta 130 Da Aka Sace A Jihar Neja  Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.