Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maikaba Ya Yi Murabus A Matsayinsa Kocin Wikki Tourist FC Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • NEDC : Zata Samar Da Cikekken Kulawa Wa ‘Yan Jaridar Da Sukayi Hatsari A Bauchi Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Trump Zata Kafa Kasuwar Ma’adanai Amurka
  • An Yanke Mishi Hukuncin Kisa Saboda Neman Kudin Aure Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Babban Malamin Musulunci Sheikh Usman Kusfa Zaria Ya Rasu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

‘Yan Jarida Sunyi Mummunan Hatsari A Bauchi
Published: February 6, 2026 at 12:57 PM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: February 6, 2026

Daga Ahmad Muhammad,Bauchi

‘Yan jarida kimanin su 14 da suka fito daga kafafen yada labarai dabam -dabam suka gamu da mummunar hatsarin mota a yayin da suke cikin tawagar hukumar raya yankin Arewa Maso Gabas (NEDC)

Shugaban kungiyar Yan Jarida Na kasa reshen jihar Bauchi da ke Arewa maso gabashin Najeriya Kwamred Umar Said ya tabbatar da aukuwar lamarin.

Umar Said wanda yake jagorantan aikin  yace tare suke tafiya , direban motar Yana gudu Sai taqwace ta Tashi sama ta shiga daji kafin daga bisani tayi ta dungure dasu tana zubar da mutanen da ke ciki har Allah ya tsaida su.

Ya nuna godiya wa Allah saboda ba a rasa rai ko daya ba a ciki amma an Samu munanan raunuka da asarar kayayyakin Aiki”

Ya godewa Ministan Uba Maigari Ahmadu , da Mataimakin Gwamnan Jihar Bauchi Muhammadu Awwal Jatau, da Shugaba da Manajin Darektan Hukumar NEDC sauran Ma’aikatan Hukumar da ‘Yanjaridu saboda yadda suka nuna damuwarsu kan abinda ya faru da Kuma yadda suka tsaya Kan lamarin.

Lokacin da abin ya faru Yan jaridun suna tafiya ne a ƙarƙashin jagorancin ƙaramin ministan raya yankuna, Alhaji Uba Maigari Ahmadu a yayin da suke yawon buɗewa da miƙa ayyukan da hukumar NEDC ta gudanar a jihar Bauchi zuwa hannun gwamnatin jihar.

Hatsarin ya faru ne a kan titin Yashi zuwa Yelwan Duguri da ke cikin ƙaramar hukumar Alkaleri a jihar Bauchi da ke tarayyar Najeriya a yau ranar Jumma’a, bayan ministan ya qaddamar da katafaren makaranta a garin Yalwan Duguri.

‘yan jaridun sun samu munanan raunuka raunuka daban-daban yayin da ake ƙoƙarin samar musu da agajin gaggawa a asibitin Yelwan Duguri daga bisani kuma za a wuce da su babban asibiti a Bauchi domin neman musu kulawar likitoci.

‘Yan jaridun da abin ya Shafa waɗanda suka fito daga gidajen talabijin na Channels, AIT, NTA, BATV,Arise da wasu irin su wakilan manyan jaridun na Guardian, the nation, kamfanin dillancin labarai Na Nijeriya (News agency of Nigeria) (NAN) da sauransu da dama.

Hatsarin ya faru ne jimkaɗan bayan da tawagar suka buɗe aikin makarantar GSS a Yelwan Duguri inda suke kan hanyarsu ta zuwa domin buɗe wasu ayyukan.

Daga cikin waɗanda suke cikin tawagar har da minista, shugabannin NEDC, chairman da MD, mataimakin gwamnan jihar Bauchi da sauransu.

Kazalika, Wakilinmu wanda ke cikin tawagar ya shaida mana cewa motar da ta gamu da hatsarin ɗaya ce daga cikin motocin da ‘yan jaridan ke amfani da su a yayin aikin ɗauko labarin. Ya kuma tabbatar mana da cewa kayayyakin aikin jarida dama kamar su Kamarori sun lalace. Amma Babu asarar rai.

Labarai, Najeriya

Post navigation

Previous Post: Jakadan Amurka A Poland Ya Yanke Hulda Da Kakakin Majalisar Kasar
Next Post: Tawagar Shirya Gasar Kwallon Sarakuna A Gombe Ta Ziyarci Masarautun Jihar

Karin Labarai Masu Alaka

Wasu Muhimman Abubuwa Da Najeriya Ba Zata Manta Da Su Ba A 2025 Labarai
Kamfanin Hakar Ma’adanai Na Kasar Kanada Ya Cigaban Da Aikinsa Labarai
Gwamnatin Gombe Ta Kulla Yarjejeniyar Da New Zealand Kimiya
SERVICOM, ATBUTH Ta Cafke Wani Da Ake Zargin Dan Damfara Ne Labarai
Ana Cigaba Da Samun Hare Hare Da Jiragen Marasa Matuki A Sudan Labarai
Tinubu Ya Buƙaci Gwamnoni Su Mutunta Hukuncin Kotun Ƙoli Kan ’Yancin Kuɗin ƙananan Hukumomi Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • ‘Yan Bindiga Sun Karya Alkawarin Dakatar Da Kai Hare Hare A Najeriya
  • Amurka Zata Bawa Sojojin Najeriya Horo
  • Indonesia Zata Kafafa Rundunar Kiyaye Zaman Lafiya A Gaza
  • Shugabannin Kasar Australia Sun Bukaci ‘Yan Kasar Suyi Zanga Zanga Cikin Lumana
  • Shugaban Afrika Ta Kudu Yanuna Goyon Bayan Kawo Karshen Yaki Tsakanin Rasha Da Ukraine

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Kasar Ukraine Ta Yabawa Tarayyar Turai Bisa Bata Tallafi Labarai
  • Rahoton MDD Yace An Kashe Fiye Da Farar 1000 A Sudan Labarai
  • Yanbindiga sun Kashe mutun guda tare da yin garkuwa da mutane kimanin 100 a Jihar Nejan Najeriya. Najeriya
  • Matatar Man Dangote Zata Wadatar Da Najeriya Da Makota Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Gwamnatin Tinubu Zata Gyara Hanyar Akwanga Zuwa Jos Labarai
  • Amurka Ta Kama Wani Jirgin Dakon Mai Amurka
  • An Shirya Taron Horas Da Matasa Gabanin Wasan Motsa Jiki 2025 Wasanni
  • Yajin Aikin Ma’aikatan Lafiya Na Shafar Harkokin Jinya A Asibitoci Kiwon Lafiya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.