Kasar Netherlands ta mayawar da kasar Masar kan wani mutum-mutumi na tarihi da aka sace mata, wanda aka sassaka kimanin Shekaru 3,500 da suka wuce, bayan da ya bayyana a wani taron bajakolin kayan fasaha da aka gabatar a shekarar 2022.
Wani bincike da ‘yan sanda da kuma masu bin diddigin kayan al’adun gargajiya ya nuna cewa an sato mutum -mutumin ne, kuma aka dauke shi daga kasar Masar, me yiwuwa lokacin tashin-tashinar da aka yi a yankunan Masar, Libya, Tunisia, Sham, Yemen da Bahrain, kafin a yi baja kolin shi a kasuwar kasashen waje.
Masana suna da yakinin cewa kan mutum-mutumin ya samo asali ne dga garin Luxor a kudancin Masar, yana kuma nuni da wani babba a gwamnati sarki Thutmose na 3.


