Aljeriya ta fara soke yarjejeniyar zirga zirgar jirgin sama tsakaninta da hadaddiyar daular larabawa, wacce kasashen suka rantabawa hanu cikin watan mayun shekara ta 2013, kamar yadda aka ji daga kafofin yada labaran kasar a ranar Asabar.
Ba’a bada bayani kan dalilin nan da nan kan daukar wanan mataki ba, amma kafofin yada labaran kasar na matukar sukar hadaddiyar daular larabawan a cikin watannin baya bayan nan kan zargin kasar tana neman haddasa husuma a yankin.
A cikin sanarwar da gidan rediyon kasar ya bayar, yace, “Aljeriya ta fara daukar matakan kawo karshen yarjejeniyar da kasashen biyu suka kulla game da zirga zirgar jirgin sama tsakanin kasashen biyu, da aka yi cikin watan mayun shekara ta 2013, daga bisani aka karfafa shi tare da dokar shugaban kasa cikin watan Disamba 2014.”
Hadaddiyar daular larabawan dai bata furta komi ba game da wannan sanarwa.
A cikin watan oktoban bara, shugaban kasar Aljeriya Abdelmajid Tebboune yace aljeriya tana da kyakkyawar dangantaka da kasashe dake yankin Gulf, in banda kasa daya, a zaman gugar zana ga hadddiyar daular larabawa.
Ya zargi kasar da bai bayyan sunanta ba, da yin shishshigi cikin harkokin cikin gidanta da nufin sukurkuta harkokin kasar.


