Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u Afrika
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa Afrika
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa Afrika
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa Afrika
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed Afrika

Iran Tace Farisa Zata Kai Hari Kan Mayakan Amurka
Published: February 8, 2026 at 10:16 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Ministan harkokin wajen Iran ya fada ranar Asabar cewa, Farisa zata kai hari kan sansanonin mayakan Amurka da suke gabas ta tsakiya, ministan wanda yayi magana ranar Asabar yace kada a dauka matakin a zaman kai hari ga kasashen da suka bada masauki ga dakarun na Amurka ba.

Ministan harkokin wajen Abbas Araqchi, wanda yayi magana da tashar talabijin ta Aljazeera, kwana daya bayan da hukumomin Iran da Washington suka ce za su ci gaba da tattaunawar da suke yi ba kai tsaye ba, game da shirin Nukiyar kasar, tattaunawar da duka bangarorin biyu suka yaba dashi a zaman da suka yi a ranar jumma’a a Oman.

Araqchi yace ba’a tsaida rana domin ci gaba da tattaunawar ba, amma shugaba Trump yace za’a yi zagaye na biyu na shawarwarin a farkon mako mai zuwa, ministan harkokin wajen yace duka sassan biyu sun amince da yin haka ba tare da bata lokaci ba.

Shugaba Trump yayi barazanar zai kai wa Iran hari bayan da Amurkan ta jibge jiragen yakin ruwa a yankin, inda ta bukaci Iran ta daina sarrafa ma’adinan Uranium, da zai bata damar kera makamin Nukiya, da kuma tsaida kera makamai masu linzami, da kuma ta daina bada goyon bayan da take yi ga kungiyoyin ‘yan tawaye a yankin.

Yayinda duka sassan biyu suka nuna a shirye suke su farfado da shawarwari kan shirin nukiliyar kasar da take rigima da kasashen yamacin duniya akai, Araqchi yaki ya amince a fadada batutuwa da shawarwarin zai taba.

Amurka, Labarai

Post navigation

Previous Post: Kasar Aljeriya Ta Soke Yarjejeniyar Jirgin Sama Tsakaninta Da Daular Larabawa
Next Post: Anyi Janazar ‘Yan Shi’a 33 Da Aka Kashe A Masallacin Juma’a

Karin Labarai Masu Alaka

Tinubu Na Kokarin Rage Tsadar Sufuri Ta Hanyar Shirin CNG Afrika
Bankin Duniya Zaibawa Kasar Mozambique Lamunin Dala Bilyan Shida Labarai
‘Yan Tawayen M23 Masu Samun Goyon Bayan Rwanda Basu Jamye A Ulvira Ba Labarai
Za’a Fuskanci Bala’in Yunwa A Najeriya Labarai
Kenya Ta Cimma Yarjejeniya Da Kasar Rasha Afrika
Kocin Zambia Na Mata Ba Lafiya Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Kira Ga Haɗin Kai Domin Bunƙasa Maɗaba’u
  • Mataimakin Shugaban kasar Najeriya Ya Kaddamar Da Taron Zuba Jari A Jihar Jigawa
  • Uwargidan Shugaban Ƙasar Najeriya Ta Ƙaddamar Muhimman Ayyuka A Jihar Jigawa
  • Gwamnatin Najeriya Ta Fara Aikin Babbar Hanyar Da Za Ta Haɗa Jihohin Arewa
  • Gwamnatin Benue Da MACBAN Sun Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Ardo Risku Mohammed

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Gwamna Zulum: Ya Bukaci Sojoji Su Cigaba Da Yakar Boko Haram Da ISWAP Labarai
  • Jakadan Amurka A Poland Ya Yanke Hulda Da Kakakin Majalisar Kasar Labarai
  • Kungiyar ‘Yan Jarida Ta Najeriya Ta Tabbatar Da Kyautata Rayuwar Mambobin ta Labarai
  • Najeriya Ta Mika Koke Ga FIFA Tana Zargin DR Congo Ta Sanya ‘Yan Wasan Da Basu Cancantaba Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Tinubu Yace Zayyi Hadaka Da Kasashen Duniya Domin Kawo Karshen Rashin Tsaro. Najeriya
  • Shugaban Lebanon Ya Nemi Gudanar Da Shawarwari Kai Tsaye Afrika
  • Gwamnatin Trump Tana Cigaba Da Korar Baki Daga Amurka Afrika
  • Gwamnatin Tinubu Zata Gyara Hanyar Akwanga Zuwa Jos Labarai
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.