Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Gamayyar ADC Ta Bukaci Shugaban INEC Ya Yi Murabus Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida (NUJ) A Bauchi Ta Yi Allah Wadai Da Mummunan Harin Da Jami’an ‘Yan Sanda Suka Kai Wa Daya Daga Cikin Mambobinta Labarai
  • An Kwace Nasarar Da Senegal Tayi na (CAF) An Ba Wa Maroko Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Zelensky: Gabas Ta Tsakiya Na Iya Nuna Makomarmu Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Mojtaba Khamenei Ya Zama Sabon Jagoran Jamhuriyar Musulunci ta Iran Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu

Iran Tace Farisa Zata Kai Hari Kan Mayakan Amurka
Published: February 8, 2026 at 10:16 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Ministan harkokin wajen Iran ya fada ranar Asabar cewa, Farisa zata kai hari kan sansanonin mayakan Amurka da suke gabas ta tsakiya, ministan wanda yayi magana ranar Asabar yace kada a dauka matakin a zaman kai hari ga kasashen da suka bada masauki ga dakarun na Amurka ba.

Ministan harkokin wajen Abbas Araqchi, wanda yayi magana da tashar talabijin ta Aljazeera, kwana daya bayan da hukumomin Iran da Washington suka ce za su ci gaba da tattaunawar da suke yi ba kai tsaye ba, game da shirin Nukiyar kasar, tattaunawar da duka bangarorin biyu suka yaba dashi a zaman da suka yi a ranar jumma’a a Oman.

Araqchi yace ba’a tsaida rana domin ci gaba da tattaunawar ba, amma shugaba Trump yace za’a yi zagaye na biyu na shawarwarin a farkon mako mai zuwa, ministan harkokin wajen yace duka sassan biyu sun amince da yin haka ba tare da bata lokaci ba.

Shugaba Trump yayi barazanar zai kai wa Iran hari bayan da Amurkan ta jibge jiragen yakin ruwa a yankin, inda ta bukaci Iran ta daina sarrafa ma’adinan Uranium, da zai bata damar kera makamin Nukiya, da kuma tsaida kera makamai masu linzami, da kuma ta daina bada goyon bayan da take yi ga kungiyoyin ‘yan tawaye a yankin.

Yayinda duka sassan biyu suka nuna a shirye suke su farfado da shawarwari kan shirin nukiliyar kasar da take rigima da kasashen yamacin duniya akai, Araqchi yaki ya amince a fadada batutuwa da shawarwarin zai taba.

Amurka, Labarai

Post navigation

Previous Post: Kasar Aljeriya Ta Soke Yarjejeniyar Jirgin Sama Tsakaninta Da Daular Larabawa
Next Post: Anyi Janazar ‘Yan Shi’a 33 Da Aka Kashe A Masallacin Juma’a

Karin Labarai Masu Alaka

Kudin Man Fetur Ya Karu Da Kashi 10 Cikin 100 Afrika
Kasar Ghana Zata Sauya Inda Take Kai Sarrafa Gwal Afrika
Jakadan Amurka A Poland Ya Yanke Hulda Da Kakakin Majalisar Kasar Labarai
Sojojin Faransa Sun Karyata Zargin Bobi Wine Labarai
Kasar Gabon Ta Nemi Tallafin Asusun Bada Lamuni Na IMF Afrika
Ukraine Tana Cigaba Da Tattaunawa Da Amurka Domin Kawo Karshen Yakin Kasar Amurka

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Wani Dan Ta’adda Ya Hallaka ‘Yan Makaranta A Kasar Uganda
  • Sakataren Tsaron Amurka Ya Kori Shugaban Sojin Kasar
  • Kwararru Sun Nuna Damuwa Game Da Yakin Iran
  • Za’a Kada Kuri’a A Kwamitin Tsaro Na MDD Kan Yaki
  • Kasashen Da Dama Na Neman Hanyar Cigaba Da Dakon Makamashi

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Hukumar Tsaron Civil Defence A Gombe Ta Samar Da Jami’ai Don Tabbatar Da Tsaro A Bukukuwan Karshen Shekara Labarai
  • Shugaban Kasar Iran Yace Kasar Bata Da Kiyayya Tsakaninta Da Amurkawa Afrika
  • Suvr Jahun: Ya Kamata Obasanjo Ya Bar Al’umar Ƙasa Su Fito Da Wadda Suke So 2027 Najeriya
  • Mutane Da Yawa Ke Mutuwa A Dalilin Shan Magani Ba Bisa Ka’ida Ba Kiwon Lafiya
  • Afirka Ta Kudu Ta Bayyana Yadda Aka Yaudari ‘Yan Kasar Ake Tilasta Musu Ayyukan Bauta Afrika
  • Gwamnonin Arewa Sunyi Allah Wadai Da Harin Jos Afrika
  • Tinubu Ya Buƙaci Gwamnoni Su Mutunta Hukuncin Kotun Ƙoli Kan ’Yancin Kuɗin ƙananan Hukumomi Labarai
  • Kungiyar MDD Ta Bukaci Ayi Bincike Game Da Kashe ‘Yan Iran Sauran Duniya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.