Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani Afrika
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027 Afrika
  • Najeriya: Gombe ‘Yan Sanda Sun Kammala Bikin Ranar Matasa Da Dasa Itatuwa Domin Makoma Mai Ɗorewa Afrika
  • Inuwa Yahaya Zai Jagoranci Tattara Masu Ruwa da Tsaki Na APC A Arewa Maso Gabashin Najeriya Afrika
  • APC Ta Tsayar Da Usman Maijama’a Kallamu A Zaɓen Cike Gurbi Na Gombe, Kwami Da Funakaye Afrika

Iran Tace Farisa Zata Kai Hari Kan Mayakan Amurka
Published: February 8, 2026 at 10:16 AM | By: Aliyu Bala Gerengi

Ministan harkokin wajen Iran ya fada ranar Asabar cewa, Farisa zata kai hari kan sansanonin mayakan Amurka da suke gabas ta tsakiya, ministan wanda yayi magana ranar Asabar yace kada a dauka matakin a zaman kai hari ga kasashen da suka bada masauki ga dakarun na Amurka ba.

Ministan harkokin wajen Abbas Araqchi, wanda yayi magana da tashar talabijin ta Aljazeera, kwana daya bayan da hukumomin Iran da Washington suka ce za su ci gaba da tattaunawar da suke yi ba kai tsaye ba, game da shirin Nukiyar kasar, tattaunawar da duka bangarorin biyu suka yaba dashi a zaman da suka yi a ranar jumma’a a Oman.

Araqchi yace ba’a tsaida rana domin ci gaba da tattaunawar ba, amma shugaba Trump yace za’a yi zagaye na biyu na shawarwarin a farkon mako mai zuwa, ministan harkokin wajen yace duka sassan biyu sun amince da yin haka ba tare da bata lokaci ba.

Shugaba Trump yayi barazanar zai kai wa Iran hari bayan da Amurkan ta jibge jiragen yakin ruwa a yankin, inda ta bukaci Iran ta daina sarrafa ma’adinan Uranium, da zai bata damar kera makamin Nukiya, da kuma tsaida kera makamai masu linzami, da kuma ta daina bada goyon bayan da take yi ga kungiyoyin ‘yan tawaye a yankin.

Yayinda duka sassan biyu suka nuna a shirye suke su farfado da shawarwari kan shirin nukiliyar kasar da take rigima da kasashen yamacin duniya akai, Araqchi yaki ya amince a fadada batutuwa da shawarwarin zai taba.

Amurka, Labarai

Post navigation

Previous Post: Kasar Aljeriya Ta Soke Yarjejeniyar Jirgin Sama Tsakaninta Da Daular Larabawa
Next Post: Anyi Janazar ‘Yan Shi’a 33 Da Aka Kashe A Masallacin Juma’a

Karin Labarai Masu Alaka

Gwamnatin Tinubu Zata Samar Da Wutan Solar A Jami’ar ADUST Wudil Afrika
Anakan Bincike Wajen Gano Dan Bindigar Da Ya Kashe Dalibai Biyu A Jihar Rhode Island Amurka
Hukumar DSS Ta Sake Kama Abubakar Malami Labarai
Gwamnatin Tinubu Ta Karyata Kafa Kamfanin Gwal A Legas Labarai
Dakarun Gwamnatin Kasar Sham Tayi Mamaya Zuwa Gabashin Kasar Labarai
Gwamnatin Najeriya Tace Ta Farmaki Mayakan ISIS A Jihar Sokoto Labarai

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Magoya Bayan Liverpool Sun Bukaci Iraola Ya Ɗauki Mataki Mai Tsauri Kan Szoboszlai
  • Tottenham Tana Da Damar Ɗaukar Ɗan Wasan Gefe Na Chelsea, Mykhailo Mudryk.
  • Maryam Dan’azumi Ta Koma Gida Bayan Zama Gwarzuwar Gasar Alƙur’ani
  • Goje Yace Bai Sauya Sheka Ba, Yana Shawara Kan Makomar Siyasar 2027
  • Nigeria Ta Samu Tikitin Gasar Wasan Beach Volleyball A Olympics Los Angeles 2028

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Wani Dan Bindiga Ya Harbi Dakarun Tsaron Cikin Gida Su Biyu A Washington DC Labarai
  • Kasar Ghana Zata Sauya Inda Take Kai Sarrafa Gwal Afrika
  • Dan Wasan Gaba Na Manchester United, Zirkzee Ya Amince Da Komawa Juventus Ko Napoli Wasanni
  • Shugaban Trump: Washington Zatayi Cinikayya Da Indiya Amurka
  • Kasar Amurka Da Rasha Zasu Kawo Karshen Tsagaita Nukiliya Amurka
  • Tantance Gaskiyar Bayanai Shi Ne Ginshiƙin Aikin Jarida Mai Nagarta – Abdulaziz Afrika
  • Tinubu: Zamu Kara Kyautata Samar Da Kayan Aiki Ga Jami’an Tsaro Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Fiye Da Mutane 50 Tare Da Sace Mata Da Yara A Jihar Zamfara Najeriya
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.