Skip to content
Saurari Shirye-shiryenmu
  • Game Da Mu
  • Talla
  • Tuntube Mu
GTA Hausa Logo

GTA Hausa

Amintacciyar Murya

gtahausa Banner
  • Babban Shafi
  • Labarai
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Kiwon Lafiya
  • Najeriya
  • Afrika
  • Amurka
  • Shirye-Shirye
  • Toggle search form
  • Jarman Deba Ya Kada Senata Goje A Zaben Fidda Gwani Afrika
  • Jami’an ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayi Afrika
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai Afrika
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari Afrika
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe Afrika

Yawan Mai Da Kasashen OPEC Suke Hakawo Yayi Kasa Sosai
Published: February 10, 2026 at 10:36 AM | By: Aliyu Bala Gerengi | Updated: February 10, 2026

Yawan mai da kasashe dake kungiyar OPEC masu arzikin mai suke hakowa yayi kasa sakamakon karancin mai da Najeriya da Libya suke hakowa, kamar yadda wani bincike da kamfanin dillancin lbarai na Reuters ya gano Ranar Litinin.

Kasashe da suke cikin kungiyar OPEC suna hakar mai ganga milya 28.34 ako wace rana cikin watan Junairun da ya wuce, wanda ya nuna koma baya da kamar gangar mai dubu 60 idan aka duba alkaluman watan Disamba binciken ya nuna, Najeriya ce ta sami koma baya sosai a yawan abunda take hakowa.

OPEC da kasashe kawayenta da suka hada da Rasha sun fara rage hanu a watanni uku na farkon shekara na yawan mai da suke hakowa saboda fargabar suna iya fuskantar kwanten mai a duniya.

Karkashin wata yarjejeniyar da kasashe 8 da suke cikin kungiyar da wasu kawayenta ba zasu kara yawan abunda suke hakowa ba a watan jiya, sun hada da Aljeriya, da Iraq, da Kuwait, da saudi Arabia, da hadaddiyar daular larabawa, gabannin ganin tasirin rage abunda suke hakowa da adadinsa ya kai gangan dubu 130, da zai shafi Iraqi da kuma hadaddiyar daular larabawa.

Najeriya ce dai aka ga matukar koma bayan mai da take hakowa, da kuma Libya, wacce ta fuskanci matsalar yanayi wadda ya shafi lodin manta.

Haka nan an sami koma bayan mai daga Iran sosai, saboda Amurka tana kara mata takunkumi game da shirin Nukiliyar kasar.

Sai dai binciken bai fadi matsalar data sa Najeriya ta sami koma bayan mai da take hakowa ba.

A halinda ake ciki kuma, farashin mai ya tashi da kamar kashi daya, bayanda Amurka ta gargadi jiragen ruwa suyi taka tsantsan kusa da Iran.

Labarai, Sauran Duniya

Post navigation

Previous Post: Maikaba Ya Yi Murabus A Matsayinsa Kocin Wikki Tourist FC
Next Post: Birtaniya Ta Bukaci Israela Ta Janye Shawarar Fadada Iko Da Kogin Jordan

Karin Labarai Masu Alaka

Gobara Ta Lalata Shaguna Da Gidajen Abinci A Gombe Labarai
Kasar Mauritius Zata Rage Amfani Da Makamashi Afrika
Tattaunawar Nukiliya Tsakanin Iran Da Amurka Yana Tasirin Akan Farashin Albarkatun Mai Amurka
Kasar Spain Ta Rufe Sararin Saman Kasar Amurka
Hukumomi A Kasar Syri Lanka Suna Kokarin Fidda Jirgin Yakin Iran Daga Kasar Afrika
Jirage Marasa Matuka Sun Kaiwa Jiragen Ruwan Mai Hari A Gulf Afrika

Aiko Mana Sako Cancel reply

Kada ka damu, baza a wallafa adireshin imel dinka ba. Required fields are marked *

Sabbin Labarai

  • Jarman Deba Ya Kada Senata Goje A Zaben Fidda Gwani
  • Jami’an ‘Yan Sanda A Gombe Sun Kama Barayi
  • Kotu Ta Bada Belin Nasiru El Rufai
  • Najeriya Da Jamus Sun Kulla Yarjejeniyar Zuba Jari
  • Zaben Fidda Gwani Ya Gudana Lafiya A Jihar Gombe

Rukuni

  • Afrika
  • Amurka
  • Bidiyo
  • Kimiya
  • Kiwon Lafiya
  • Labarai
  • Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Najeriya
  • Nishadi
  • Rediyo
  • Rumbun Hotuna
  • Sana'o'i
  • Sauran Duniya
  • Shirye-Shirye
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Uncategorized
  • Wasanni
  • Yau Shekaru 60 Da Kisan Gilla Ga Sir. Ahmadu Bello Sardaunan Sakkwato Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Malaman Addinin Musulunci Da Kirista Sunyi Bikin Cika Shekara 15 Na Iftar A Najeriya Afrika
  • Tinubu, Akpabio da Ministoci 9 Zasu Tafi Ƙasar Birtaniya Afrika
  • Wani Jirgin Kasa Yayi Hatsari A Kudancin Spain Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
  • Farashin Kasuwar Yawon Bude Ido A Kasuwar Hannayen Jari Ya Fadi Afrika
  • Tsohon Gwamnan Kano, Malam Ibrahim Shekarau Ya Koma Jam’iyyar APC Afrika
  • Sojojin Kasar Uganda Sun Bazama Neman Bobi Wine Sakamakon Rikicin Bayan Zabe Siyasa
  • Guinea An Zabi Madugun Sojojin Da Suka yi Juyin Mulki Mamady A Shugaban Ƙasar, Labarai Da Ɗumi-Ɗuminsu
GTA Hausa Logo

Yadda Ake Amfani Da Bayanan Ku

A GTA Hausa, mun kuduri aniyar kare sirrin maziyarta shafukanmu. Wannan Tsarin Sirri yana bayyana irin bayanan da muke tattarawa, yadda muke amfani da su, da kuma zaɓuɓɓukan da kuke da su game da bayanan ku na sirri. Ci Gaba Da Karatu

Shafukan Mu

  • Facebook
  • (Twitter)
  • Instagram
  • TikTok
  • YouTube

Haƙƙin Mallaka © 2025 GTA Hausa - Dukkan Haƙƙoƙi Mallakinmu Ne.