Yawan mai da kasashe dake kungiyar OPEC masu arzikin mai suke hakowa yayi kasa sakamakon karancin mai da Najeriya da Libya suke hakowa, kamar yadda wani bincike da kamfanin dillancin lbarai na Reuters ya gano Ranar Litinin.
Kasashe da suke cikin kungiyar OPEC suna hakar mai ganga milya 28.34 ako wace rana cikin watan Junairun da ya wuce, wanda ya nuna koma baya da kamar gangar mai dubu 60 idan aka duba alkaluman watan Disamba binciken ya nuna, Najeriya ce ta sami koma baya sosai a yawan abunda take hakowa.
OPEC da kasashe kawayenta da suka hada da Rasha sun fara rage hanu a watanni uku na farkon shekara na yawan mai da suke hakowa saboda fargabar suna iya fuskantar kwanten mai a duniya.
Karkashin wata yarjejeniyar da kasashe 8 da suke cikin kungiyar da wasu kawayenta ba zasu kara yawan abunda suke hakowa ba a watan jiya, sun hada da Aljeriya, da Iraq, da Kuwait, da saudi Arabia, da hadaddiyar daular larabawa, gabannin ganin tasirin rage abunda suke hakowa da adadinsa ya kai gangan dubu 130, da zai shafi Iraqi da kuma hadaddiyar daular larabawa.
Najeriya ce dai aka ga matukar koma bayan mai da take hakowa, da kuma Libya, wacce ta fuskanci matsalar yanayi wadda ya shafi lodin manta.
Haka nan an sami koma bayan mai daga Iran sosai, saboda Amurka tana kara mata takunkumi game da shirin Nukiliyar kasar.
Sai dai binciken bai fadi matsalar data sa Najeriya ta sami koma bayan mai da take hakowa ba.
A halinda ake ciki kuma, farashin mai ya tashi da kamar kashi daya, bayanda Amurka ta gargadi jiragen ruwa suyi taka tsantsan kusa da Iran.


